Mafarkin Kunama

    Slm mlm barka da juma at dafatan katashi lfy mlm muna godiya Allah yasaka da alkairi mlm nayi mafarkin naga kunama amakaranta munazaune sai na ga kunama yahuce Amma yan ajin basuganiba sai yabuya tajikin wani kujera sai natashi dan in yafito inkace saiga kanina yazo karban abu awajena sai kunaman yafito dagudu sai yashige rigan kanina saina fara ihu inakunama kunama sai malamimu ya tashi ya ce aina sai kanina yafa kuka sainace yashi rigan adnan sai aka fara guduwa sai malamin yamaso kusan da shi sai yadaga rigansa saiyaga kunaman yamutu saina farka a baccin amma kafin nafaka naga yadena kukuka kamar babu abin da yasamaishi mlm nasha kashe kunama agidanmu amma bantaba ganin mai girma kamar wanda nagani amafarkinaba mlm dan Allah mai hakan yake nufi

    AMSA

    Waalaikumussalam. Warahmatullahi. Wabarakatuhum.

    Imam Muhammad Ibn Seerin (Dalibin Imam Maleek) a cikin littafinsa "Kamus din Mafarki" ya ce:

    Mafarkin kunama ta hau kan mutum na nufin luwadi, mafarkin kunama ta shiga riga ko kantin mutum na nufin musiba a rayuwar mutum, ganin kunama na nufin  magulmaci ko maqiyi a cikin dangi, ganin kunama ta fito ta inda mutum yake kashi na nufin haihuwar yayan da zasu zamo maqiyansa, kashe kunama a mafarki na nufin mutum zai gano maqiyansa kuma zai ga bayansu ta fuskar qiyayyar da suke masa, harbin kunama a mafarki na nufin harshen mutum

    SHARHI:

    A shawarce ku sa ido sosai akan yaron ta hanyar nesantashi da abokan banza wadanda ka iya janyoshi zuwa ga mummunar dabi'ar mutanen Annabi Lud AS

    Sannan kuma duk sanda kunama ta harbi wani a lokacin kina kusa da wanda ta harba saiki tuno da addu'ar da Annabi SAW ya koyar wadda mutum zai dafa wajen da ta harbeshi ya karanta "Bismillah" sau 3 sannan ya ce "Audhu biqudratihi min sharri ma'ajidu wa'uhadhiru" sau 7 a tofa a wajen, in sha Allahu za a samu sauqi

    (Hadisin yana cikin Sahih Muslim mai lambata 2202)

    Sannan ki dinga koyawa qannenki da yan uwanki addu'ar har sai sun haddace kuma kice kada su dinga wasa da adhkar na safiya da maraice

    Sannan kuma a lazimci addu'a domin kuwa tana sauya qaddara kamar yanda aka rawaito

    An karbo daga Abu Hurairah RTA, Annabi SAW ya ce: "Babu abin da yake canza qaddara sai addu'a"

    Tirmidhi 3573

    Subhanakallahumma wabi hamdika, ash-hadu anla ilaha illa anta, astaghfiruka wa'atubi ilay

    Amsawa:

    ✍️Usman Danliti Mato Usmannoor_As-salafy)

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.