Nafila A Bayan Jumma’a

    𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

    Assalamu Alaikum. Menene matsayin nafilar da waɗansu suke yi a bayan Jumma’a? Raka’a nawa ne?

    𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

    Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul Laah.

    A cikin hadisi Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:

    « مَنْ كَانَ مِنْكُمْ مُصَلِّيًا بَعْدَ الْجُمُعَةِ فَلْيُصَلِّ أَرْبَعًا »

    Cikinku duk wanda zai yi sallah a bayan Jumma’a, to ya yi salah raka’o’i huɗu. (Sahih Muslim: 2075)

    Sannan kuma Abdullaah Bn Umar (Radiyal Laahu Anhumaa) ya ce:

    وَكَانَ لاَ يُصَلِّى بَعْدَ الْجُمُعَةِ حَتَّى يَنْصَرِفَ فَيُصَلِّى رَكْعَتَيْنِ

    Kuma Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya kasance ba ya yin sallah a bayan Jumma’a har sai ya juya, sai ya yi sallah raka’a biyu. (Sahih Al-Bukhaariy: 937)

    Daga waɗannan riwayoyin guda biyu ya bayyana cewa: Ya halatta mutum ya yi nafila raka’a biyu ko huɗu a bayan Jumma’a.

    WALLAHU A'ALAM

    Sheikh Muhammad Abdullaah Assalafiy

    Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

    https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.