Shin Ya Halatta Mace Tayi Abin Da Zata Mallake Mijinta Ko Saurayinta?

    𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

    Assalamu alaikum malam ya fama da jama'a Allah ya taimaka, Tambayata itace ya halatta ga mace tayi abin da zata mallake mijinta ko saurayinta?

    𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

    Ya halatta matar Aure ko budurwa ta mallake mijinta ko saurayinta, Wanda zai aureta. Musamman ma mace mai aure, ya zama wajibi ta mallake mijinta. Amma ta hanyar da babu sihiri ba, ba tsafi, ba dawo, ba Tsubbu, ba yaudara, ba nuna masa Abin da ba shine a zuciyarki ba.

    Sai dai ki Mallakeshi ta hanyar kyautatawa, bin umarninsa, amfani da kuɗin ki wajen kyautata masa, yimasa magana mai daɗi, Nuna masa tsabar gaskiya a cikin Zantukanki da Ayyukanki da shigar ki da mu'amalar ki da dai sauransu.

    Allah ta'ala yasa mudace

    WALLAHU A'ALAM

    Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://chat.whatsapp.com/FmJ5Ojsns1KFolTP8qu9GT

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

    https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.