Ko da So... (Kashi na 17)

    In kin Karanta ki yi sharing please

    "Bafa ma ganin comment din ku anya kuwa?"

    Ban iskar da aka samu kwana biyu ba tare da anyi ruwa ba ya sanya garin yin zafi, wannan ya sa da yawan mazan unguwar firfitowa kama daga matasa har dama maginta ko ina ka bi cikin unguwar maza za ka gani wasu bisa bencina wasu bisa tabarmi kowa da abin da yake, can gefen kwata bakin wani kanti bencin su Muktar ne shida abokan sa da suke zaune gefen teburin da Ibrahim ke saida kaza soyayyiya, kilishi, da dambun nama.

    Nasir da ya Æ™ara so wurin É—auke da katuwar baÆ™ar leda ne ya zauna Æ™arshen bencin tare da faÉ—in "wash! Allah yau na gaji da yawa" Salisu ne ya É—an leÆ™o kai "kai dai walllahi ka cika ragon ta in ba haka maine abin gajiya a wannan ‘yar ledar da ka É—auko?"

    Hararar sa Nasir ya yi "ai gwamma ni da baki kawai na ce na gaji kai na tabbatar sai dai kama faÉ—i wanwar"

    Muktar ne ya sa dariya "kai dai Nasiru baka mutunci mai ka mai da Salisun ne?"

    Nasir bai ba shi amsa ba ya hau fito da atamfofi cikin leda yana faÉ—in " Haja ce na kawo muku dukan mu na san kayan aure muke haÉ—awa"

    Ibrahim da ke gaban glass É—in da kayan sana'ar suke yana zubawa matashin saurayin da ya zo siyan dambun nama da doya ne ya yi caraf ya ce inason jar can zatawa Fiddausi na kyau" ya faÉ—a yana ninke takardar da ya zuba doya.

    Salisu ne ya zuro hannu zai É—auka Nasir ya yi caraf ya ce "koda ba shi ba ni baka, kuÉ—i hannu nake bawa marasa sana'a"

    " Kut.. wai mai kuka mai da ni ne?" Salisu ya faÉ—a a fusace.

    Ibrahim da ya komo ya zauna ne ya ɗauki jar da ya ce yana so yana ƙara ɗaga ta cikin hasken street light "anma atamfar nan ta yi kyau, bama zan sa a lefe ba gobe zan kai mata, in haɗa mata da kwanukan da tayo min cin cin" ɗan juyowa ya yi ya kalli Salisu mutumina kabi shawarar Muntari ka kama sana'a walllahi"

    Banza Salisun ya masa tare da ci gaba da ƙoƙarin kama tasha a radiyon sa.

    Nasir ne ya taÉ“o Muktar da tun da aka fara batun kayan baice komai kan su ba ya ce " ya mutumina ban ga kafa É—auka ba?" Murmushi Muktar ya yi abin ai na masu ‘yan mata ne.

    Nasir ne ya ɗago wata golden ɗin atamfa ya ɗora kan cinyar Muktar wannan ko fara ko baƙa za ta mata kyau ina faɗa ma, kama daina wayancewa ni namiji ne na san duk nunƙufurcin mutun dole akwai wadda yake ɗan tayawa"

    Kallon atamfar da ke cinyar sa ya yi, bai ankara ba zuciyar sa ta fara zayyano masa Hafsa cikin atamfar cikin sauri ya mayarwa da Nasir kan cinyar sa, " aiko kai namijin ƙarya ne tun da dai baka san da irin mu ba wanda sam soyayya ba ta gaban su"

    Dariya Nasir ya sa tare da mayar masa atamfar " ka rantse da Allah babu wadda kake so"

    Shiru Muktar ya yi tare da shan kunu, Salisu ne ya zuro kai "ka rantse mana" ya faÉ—a yana tsare Muktar da idanu.

    Tsuke fuska Muktar ya kumayi lokacin guda zuciyar sa na ayyano masa Hafsa yanzu da ya yi tunani mai zurfi ya fahinci ba wai iya burgeshi yarinyar kawai take ba, har da ɓurɓushin so duda shiɗin baisan ya son yake ba.

    " Sabida mai zan rantse, abin da na sani shi ne dai kawai ba wanda nake so"

    "Wai kana nufin wannan tsuke fuskar zai sa in ƙyale ka," Salisu ya faɗa tamkar da shi aka fara musun tun asali.

    "To karma ka kyale ni mana" Muktar ya faɗa, nefa da yaran da ke ɗan wasa tsakanin hanya suka faɗa suna tsalle ya bawa Muktar damar miƙewa bayin Allah sai da safen ku dama zafi ya fito dani"

    Nasir ne ya yi saurin miƙewa ya danƙa masa atamfar kaban kuɗin ƙarshen wata," numfashi ya furzar tare da kallon atamfar kamar zai maido masa da ita sai kuma ya juya ya yi gida.

    Wutar nefan da aka kawo ta haske tsakar gidan su Inna na zaune tana kwaɓin fanke Juwairiyya na Feraye kabewa ya san ta abincin safen gobe ce ya yin da Hajara ke rubutu ya yi sallama kusan dukkanin su suka amsa.

    Hajara ta É—ago ne ta ce "lah yaya mai ka siyo?"

    Hajara ta tambaya cewa ya yi "Idon matambayi," Juwairiyya tasa dariya inda Hajara ta yi ƙas da kai tana zumɓura baki. Gefen Inna ya aje ledar tare da faɗin "Nasiru ke siyar wa na ɗaukan miki wannan in kalar ba ta miki ba sai ince ya kawo ki zaɓa"

    Da rawar jiki Inna ta buÉ—e "kai masha Allah, ai ta yi sosai gabaki É—aya suka faÉ—a, albarka Inna ta hau sa masa tamkar ya siya mata duniyar nan ya yin da shi kuma yake ta faman murumushi da faÉ—in "Amin"

    ÆŠakinn sa ya shige yana sauraron Addu'oin da Innar ke masa idanun sa bisa fanka da ke kaÉ—awa baima san sa'adda bacci ya yi gaba da shi ba.

    ***

    Tunanin yadda za ta iya koyan electricity and magnetism É—innan ne duk ya cika mata rai, mafita É—aya ta faÉ—o mata shi ne Uncle Muktar, inda tasan course É—innan za ta faÉ—i É—in da gaske, da tuni tun suna hutu da take zuwa da zaman hira da suke lokacin break da tuni tasa ya fara koya mata, sai dai yanzu babu dama tun da sun koma makaranta, next week za su fara lectures gobe ko jibi take son siyi handing over da malamar da za ta rike ajin da take.

    Sam ta rasa mai yake mata daÉ—i, karatu da BUK É—in duk tabi ta tsane su, dama ba son Agric É—in nan take ba, tsaki taja ita dama art take tasan ba za a ba ta Agric ba.

    Yunwa da ta fara tambayar ta ya sa ta miƙewa ta kunna fitilar ɗakin ta dan tun da ta shigo ta yi sallah take kan daddumar ba ta ko motsa ba tun bayan sakon da ta turawa Aunty Halima, ranta sam babu daɗi ta daure ta fito falon fatan ta kar ta haɗu da kowa har zuwa gobe ta samu ta koma gidan Gwaggo.

    Hango ta da Khalil ya yi wanda yake ta fama wasa shida ƙanwar sa khairi ne ya rugo da gudu yana tsalle yana faɗin "Aunty Hafsa shi ne kika tafi kika barni ko, yau she kika dawo?"

    Jin Khalil ya anbaci Hafsan ya sa Abba juyowa " Hajiya Hansatu ashe kina gida?" Daurewa Hafsan ta yi ta ƙaraso..

    "Abba sannu da gida" ta faÉ—a kallon ta yi damuwar da ta bayyana a fuskar ta ya sa shi shi ma damuwa kafin ya ce wani abu Momy ta fara faÉ—a.

    "Eyye sannu issasshiya, wato har kin yi girman da zaki shigo gidan nan ki kasa cemun kin dawo, eh ba laifin ki bane laifin jami'a ne eh ai dole kiji kin isa tun da kin shiga University"

    Tun É—azu da Hafsa ta gano result É—in ta take son yiin kuka ta kasa sai yanzu faÉ—an Momy duk yadda takai ga daurewa na kar kukan ya kwace mata sai da ya kufce mata, aiko kamar ta tunzura Momy ta inda ta shiga ba tanan take fita ba.

    Abba ne ya ce "Dan Allah Hadiza ki kyale ta, jarrabawar su aka sa ta samu CO ba wai faÉ—an da kike mata ne ya sa ta kukan ba" ganin da ya yi ta kuma tunzura kan Hafsan ta shagwabe daga É—an faÉ—a ta hau kuka ya sa shu faÉ—in haka, zaton sa hakan zai sa ta yi tausaya ta yi shiru bai san tunzura ta ya kuma yi ba.

    Miƙewa ta yi tana faɗa tana faɗin " retake fa kace, ke yanzu ahaka da kike cewa zakiyi medicine din, ai Allah ya taimake ni da can kike da kunya ta ishe ni, ki na dai kallon Sajida ita ce best student a faculty ɗin su"

    Takaici ne ya kuma kama Hafsa ta tsani a dinga haÉ—ata da wasu a rayuwar ta, bacin haka ai kowa da irin tasa kwakwalwar.

    Abba ne ya ce "dan Allah Hadiza ki kyale ta, bacin ma haka ai GP din ta mai kyau ne in ta dage next semester ta samu GP irin wannan CGPA É—in ta zai kyau kafin su shiga lvl two din zan wa Malamin da yake koyawa yaran mu Physics magana ya dinga zuwa gida lahadi yana koya mata har na second semester É—in da zasuyi"

    Ba wai baƙin cikin samun CO ɗin ne ya bar ta ba, a'a sai dai anbatar Muktar zai dunga zuwa gida koya mata ne ya kwantar mata da hankali, farin ciki ya ɗan samu a zuciyar ta, murmushi ta yi na gode Abba ta faɗa tare komawa wurin da ake aje abinci ta ɗiba Inda Khalil yabi bayan ta cike da murna Khairi tasa kuka Abba ya ɗauke ta ya yi ɗakin Hafsan.

    Momi ta ja tsaki sam lamarin Hafsa takaici yake bata, ko wata ba aiba Hajiya Sa'adatu mahaifiyar Hidaya ta gama cika mata baki Hidayan ba ta samu matsala ba, itama jira kawai take a kafewa su Hafsan ta take ta je ta zayyana mata, komai ta tuna oho ta kuma jan wani dogon tsakin tare da faÉ—in aikin banza...

    Rubutawa

    Aeshakhabir

    Fadimafayau

    Soyayya

    Credit: LuckyTD

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.