Hukuncin Wanda Ya Rasa Sallar Juma’a Guda Uku

    𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

    As-Salaam Alaikum Wa Rahmatul Laah. Idan musulmi ya rasa sallar Jumma’a har fiye da sau uku, menene hukuncinsa?

    𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

    Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul Laah Wa Barakaatuh.

    Ya tabbata a cikin Hadisi Sahihi cewa Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:

    « مَنْ تَرَكَ ثَلاَثَ جُمَعٍ ، تَهَاوُنًا بِهَا ، طَبَعَ اللَّهُ عَلَى قَلْبِهِ »

    Wanda ya bar Juma’a har guda uku domin wulaƙantarwa gare su, to Allaah ya rufe a kan zuciyarsa.

    (An-Nasaa’iy (1378) da Abu-Daawud (1054) suka riwaito shi, kuma Al-Albaaniy ya ce: Hasan sahih ne a cikin Sahih Abi-Daawud: 1052).

    A wani lafazin kuma ya ce:

    « مَنْ تَرَكَ ثَلاَثَ جُمَعٍ مِنْ غَيْرِ عُذْرٍ ، كُتِبَ مِنَ الْمُنَافِقِينَ »

    Duk wanda ya bar Juma’a guda uku ba da wani uzuri ba, to an rubuta shi a cikin munafuƙai.

    (Al-Albaaniy ya inganta shi a cikin Sahih Al-Jaami’i: 6144 da Sahih At-Targheeb: 729).

    Daga waɗannan hadisan da makamantansu ne malamai suka gano cewa:

    (i) Zuwa sallar Juma’a wajibi ne a kan dukkan musulmi baligi mai hankali, ɗa ba bawa ba, namiji ba mace ba, kuma mazaunin gari ba matafiyi ba.

    (ii) Haram ne mutum musulmi mai waɗancan siffofin da aka ambata ya ƙi zuwa sallar jumaa haka nan siddan, ba da wani uzuri gamsasshe ba.

    (iii) Daga cikin uzurin da ke halatta barin zuwa Juma’a in ji malamai, akwai: Rashin lafiya, ruwan sama, sanyi mai tsanani, tsoro, tafiya, bauta da kuma kasantuwar ita mace ce.

    (iv) Ƙin zuwa masallacin Jumaa haka nan kawai don wulaƙantar da alamarinta, ba da wani uzuri ko hanzari abin karɓa a Shari’a ba, ya shigar da mutum cikin jama’ar munafuƙai waɗanda kuma ake rufewa a kan zukatansu.

    Allaah ya kiyaye. Allaah ya shiryar da mu.

    WALLAHU A'ALAM

    Sheikh Muhammad Abdullaah Assalafiy

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

    https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.