Hukuncin Ƙyalle Ko Yadin Da Yakan Rage A Wurin Tela

    𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀��𝐀

    Assalamu Alaikum Wa Rahmatul Laah. Mene ne hukuncin ƙyalle ko yadin da yakan rage a wurin tela bayan ya gama ɗinka kayan da aka biya shi kuɗin aikinsa cif? Ko ya halatta ya tattara irin waɗannan ƙyallayen ya ɗinka ƙananan riguna na yara, ya riƙa sayarwa?

    𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

    Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul Laah Wa Barakaatuh.

    A asali haƙƙin musulmi ne a kan ɗan’uwansa musulmi cewa kar ya kuskura ya ci dukiyarsa sai da jin daɗin ransa. Ko da kuwa wani abu ne ƙanƙane, balle kuma wani abu babba. Allaah Taaala ya ce:

     یَـٰۤأَیُّهَا ٱلَّذِینَ ءَامَنُوا۟ لَا تَأۡكُلُوۤا۟ أَمۡوَ ٰ⁠لَكُم بَیۡنَكُم بِٱلۡبَـٰطِلِ إِلَّاۤ أَن تَكُونَ تِجَـٰرَةً عَن تَرَاضࣲ مِّنكُمۡۚ

    Ya ku waɗanda suka yi Imani! Kar ku ci dukiyoyinku a tsakanin da zalunci, sai dai idan kasuwanci ne a bisa amincewa da yarda a tsakaninku. (Surah An-Nisaa’: 29)

    Kuma Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:

    « الْمُسْلِمُ أَخُو الْمُسْلِمِ ، لاَ يَظْلِمُهُ وَلاَ يُسْلِمُهُ »

    Musulmi ɗan’uwan musulmi ne: Ba ya zaluntar sa, kuma ba ya bari a zalunce shi. (Sahih Al-Bukhaariy: 2442, Sahih Muslim: 6706)

    Wannan laifin yana ƙara girma idan ya kai shi ga yin rantsuwa domin ya ci haƙƙin musulmi da zalunci. Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:

    « مَنِ اقْتَطَعَ حَقَّ امْرِئٍ مُسْلِمٍ بِيَمِينِهِ فَقَدْ أَوْجَبَ اللَّهُ لَهُ النَّارَ وَحَرَّمَ عَلَيْهِ الْجَنَّةَ » . فَقَالَ لَهُ رَجُلٌ : وَإِنْ كَانَ شَيْئًا يَسِيرًا يَا رَسُولَ اللَّهِ ، قَالَ : « وَإِنْ قَضِيبًا مِنْ أَرَاكٍ ».

    Duk wanda ya yanke haƙiƙin wani mutum musulmi da rantsuwarsa, to tabbas Allaah ya wajabta masa shiga Wuta, kuma ya haramta masa shiga aljannah. Sai wani mutum ya tambaye shi: Manzon Allaah! Ko da wani abu ne ɗan kaɗan? Ya ce: Ko da ɗan ita cen araak ne na yin aswaki. (Sahih Muslim: 370)

    Daga nan muke fahimtar cewa:

    1. Bai halatta musulmi ya cuci musulmi ba ko da ɗan ƙanƙanen abu ne, balle kuma babban abu?

    2. Wajibi ne ya mayar masa da abin da ya cuce shi a kai, kuma ya nemi gafararsa a kan haka, bayan ya tuba ga Allaah.

    3. Idan abin ba zai samu ba a yanzu sai ya nemi ya fiyarsa kafin mutuwarsa ko mutuwarsa.

    A ƙarƙashin wannan wajibi ne tela ya tattara dukkan yankakku da gutsurarrun ƙyallayen da suka ragu, ya haɗa da ɗinkakkun tufafin ya bayar ga mai kayan. Amma idan shi da kansa ne ya yarda cewa ya riƙe waɗannan yankakkun, to shikenan.

    Sannan kuma: Idan al’adar mutane a wani gari ko wani wuri ta gudana a kan cewa, ba a dawo wa mai kaya da irin waɗannan yankakkun ƙyallayen, to babu wani laifi idan tela ya tattara irinsu ya ɗinka ƙananan kayan yara da shi.

    Kamar yadda a ƙasarmu aka saba cewa, bayan manomi ya gama kwashe amfanin gona, yana ƙyale masu roro su shiga su yi. A irin wannan roron wani kan iya samun kusan buhu guda ko ma fiye. Wannan ba laifi ba ne, matuƙar dai ba a shirya wata ciwa-ciwa domin cutar da mai gona ba, kamar a lokacin girbi a riƙa ɗiba ana ɓoyewa ko ana zubarwa da gangar.

    Don haka, a nan ma matuƙar telan bai yi wannan abin da manufar cutarwa ga mai yadin ba, ba za a ce ya yi laifi ba, muddin dai wannan yankakkun ƙyallaye ko yadin da suka bari aladarsu ce cewa ba a dawo da su.

    WALLAHU A'ALAM

    Sheikh Muhammad Abdullaah Assalafiy

    Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

    https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.