Mafarkin Kuka

    TAMBAYA (35)

    Assalamu Alaikum malan inawuni Anwuni lfy. Maln. Dan Allah miye fassarar mafarkin kuka inayawanyin mafarkin kuka Ina kuka sosai😭😭

    AMSA

    Waalaikumus salam, Warahmatullahi, Wabarakatuhum

    Alhamdulillah

    Kuka a mafarki na nufin damuwa, gajiya da hadari. Idan kuma ka yi mafarkin kana kuka saboda tsoron Allah hakan na nufin farin ciki da walwala za su zo wa mutum

    SHARHI:

    Fassarar mafarkinki na nuna cewar kin kasance cikin halin bakin ciki da damuwa wanda dayan biyune

    Immadai kina fuskantar kalubale a rayuwar aurenki wanda silar hakan kike kuka ba iya a zahiri ba harma a cikin mafarki ko kuma dai tsananin tsoron Allah da kike da shi ne ya sa idan kika tuno azabarSa kike kuka a zahiri (a farke) wanda silar hakan ya sa harma a mafarki kike kuka

    Fatana shi ne kina mafarkin kuka ne silar jin tsoron Allah da kike a fili da boye domin kuwa ya cancanci aji tsoronSa a matsayinSa na al-Khaliqu mahaliccin makaluqai

    Dalili kuwa shi ne: ina son ki kasance cikin mutane 7 wadanda Annabi SAW ya ce Allah SWT zai lullubesu a inuwarSa ranar da babu wata inuwa sai inuwar al-Arshi, wanda mutumin da shi kadai ya tuna Allah har hawaye suka zubo masa, shi ma yana cikin mutane 7 dincan

    (Bukhari da Muslim)

    Idan kuma yazaman kina kuka ne silar damuwa wadda saboda tsananinta har a mafarki ma kinayin kuka to a shawarce bai kamata ki dinga kuka ba saidai kamata ya yi ki maye gurbin kukan da yawaita fadin:

    "Hasbunallahu wani'imal wakil" da kuma "Lahaula wala quwwata illa billah"

    Ki yawaita ambaton Allah a kowanne yanayi kika tsinci kanki a ciki. Ki tuno da hadisin sahabin da ya zo wajen Annabi SAW ya ce Ya rasulullah ayyukan addini sunyimin nauyi (Sallah, Azumi, Zakkah, Aikin Hajji) Sai Annabi SAW ya ce ka jika harshenka da yawan ambaton Allah

    Sannan ki daina yawan fushi, kada ki nuna fushinki sai akan wani abu wanda ya danganci sabon Allah. Kada ki manta da hadisin bawan Allah dinnan da ya zo wajen Annabi SAW ya ce: Ya rasulullah ba ni shawara. Sai Annabi SAW ya ce kada ka yi fushi (har sau 3)

    (Sahihul Bukhari 6116)

    Muna roqon Allah SWT ya yaye mana damuwarmu ta duniya da kuma damuwar lahira

    Wallahu ta'ala a'alam

    Amsawa:

    Usman Danliti Mato, (Usmannoor_Assalafy)

    Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

    https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.