Mai Alfarma Sarkin Musulmi Muhammadu Bello Macciɗo Abubakar III

    Mai Alfarma Sarkin Musulmi Muhammadu Bello Macciɗo Abubakar III
    "Muhamman dalilin ka nis san Talata, 
    Muhamman dalilin ka niz zamni Hausa..."

    Inji Makaɗa Sa'idu Faru. Lahadi 29/10/2023 shekaru 17 Cif ke nan da wafatin Mai Alfarma Sarkin Musulmi Muhammadu Bello Macciɗo Abubakar III (Ya rasu ranar 29/10/2006 sanadiyar hatsarin/haɗarin Jirgin Saman ADC Airline a Abuja shi da sauran Bayin Allah dake cikin wannan Jirgin). An haife shi a Dange ta Jihar Sakkwato a shekarar 1926, ya bar Talata Mafara inda suka fara haɗuwa da Sa'idu Faru a matsayin Hakimi a shekarar 1956( ya zo Mafara a shekarar 1953), ya zamo Sarkin Musulmi a shekarar 1996, Allah ya karɓi abun sa a shekarar 2006. Allah ya kyauta makwanci, amin. 🤲🏾🤲🏾🤲🏾

    Daga Taskar:
    Malam Ibrahim Muhammad Birnin Magaji
    Ɗanmadamin Birnin Magaji
    Imel: birninbagaji4040@gmail.com
    Lambar Waya: 08149388452, 08027484815 

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.