Na Yi Wankan Janaba Da Sabulu Shin Alwala Ta Tananan

    TAMBAYA (40)

    Assalamu alaikum Dan Allah Ina tambaya a kan yayinda nakammala wankan janaba Kuma nasake yin wanka da sabulu alokacin shin alwalata Tananan kokuma Sena canja???

    AMSA

    Waalaikumus, Warahmatullahi, Wabarakatuhum

    Hukuncin yana damfare da tambaya, shin sabulu najasa ne ?

    Dukkan malamai sun hadu a kan cewar sabulu ba najasa ba ne ba

    Anfison a gabatarda alwalar a cikin wankan da aka yi shi da zallar ruwa mai tsarki ko kuma da soso da sabulu a maimakon ayi shi da farko kamar yanda kayi

    Wankan janaba na kamala yana dauke matsayin alwalarne ko da kuwan anyi wankan da sabulu

    A takaicedai alwalarka ta yi in sha Allahu indai har babu abin da ya faru dakai wanda yake warware alwalar

    Sannan kuma anason mutum ya sa a ransa cewar zai yi niyyar bawai don gaggawar ya yi ya gama ba ko kuma don nuna gazawa a ibada saidai anaso ya yi hakanne da kyakkyawar zuciya da kuma niyyar tsarkake jikin domin bautawa Allah SWT saboda hadisin da Abu Hurairah RTA ya rawaito cewar Annabi SAW ya ce: "Ayyuka suna karbuwane da niyya, kowanne mutum zai samu abin da ya yi niyya ne”

    Hadisan suna cikin Sahih Bukhari 1:1 (Babin Ilimi), da kuma Sahih Muslim 1:19 (Babin Imani)

    Sannan ita niyya bawai firtawa ake ba ko kuma karanta wata addu'a saidai ana yin niyya ne a zuciya

    Subhanakallahumma, wabi hamdika ash-hadu anla'ilaha illa anta astaghfiruka wa'atubi ilayk

    Amsawa:

    ✍️Usman Danliti Mato (Usmannoor_As-salafy)

    Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu. . .

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://whatsapp. com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www. facebook. com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

    https://t. me/TambayoyiDaAmsoshi

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.