Rabon Da Ya Kusance Ni Tun Kafin Azumi, Mene Ne Matsayin Auren Mu

    TAMBAYA (44)

    Aslm. Malam inada miji amma munsamu sabani abin kamar shiga tsakani ya daina kulani ya daina cin abincina inyashigo dakina a falo kantabarma yake kwana rabon da ya kusanceni tun kafin azumi meye matayin aurenmu. Wlh ban san menayi mishiba malam baya kulani kwatakwata sai dai na jisu da abokiyar zamana. Ita ce kominshi ita ce mai fada aji

    AMSA

    Waalaikumus, Warahmatullahi, Wabarakatuhum

    Aurenku yana nan daram, in sha Allah

    Saidai yana tangal tangal kuma sauran kadan shaidan ya yi nasara akanku

    Nasarar ita ce ya samu saa a kan mijinnaki ya sakeki. Babban burin shaidan ke nan, ya raba aure

    Haba, baiwar Allah, magana kikefa ta tsawon watanni 6 cur bai kusanceki ba. Wannan wanne irin laifi ne ya shiga tsakaninki da shi haka ?

    Dole akwai dalili kam

    Na farko dai ki tuna can baya a lokacinda yake sakar miki fuska kuna raha sosai

    Sannan kuma ki tuna mekikai masa wanda lokaci daya kawai ya juya miki baya

    Zata iya yiwuwa laifi kikai masa

    Sai ki sameshi a tsanake ki tambayeshi cikin siyasa

    Ni kam baban wane, me na yi maka ne na ga kwana biyu ba ka sakar min fuska

    Idan laifi na yi maka ka sanardani sai in gyara

    Kada ki sake ki yi tunanin zuwa wajen malamin duba domin kuwa a kan wannan gabarne za kiji shaidan yana raya miki kije wajen dan duba ya dubo miki dalilin sauya miki fuska da yayi

    Idan kika kuskura kika je kuwa to sallarki ta kwana 40 ba zaa amsa ba

    Don haka kamar yanda na fada miki dincan a shawarce ki kwantarda hankalinki ki tambayeshi mene ne laifin da kikai masa wanda bakisani ba har ya sa ya daina kusantarki alhalin yana mijinki halak malak

    Wallahu a'alam

    Amsawa:

    Usman Danliti Mato (Usmannoor_As-salafy)

    Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu. . .

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://whatsapp. com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www. facebook. com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

    https://t. me/TambayoyiDaAmsoshi

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.