Shin Mace Za Ta Iya Bayyana Karatu A Sallah

    𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

    Assalamu Alaikum. Mene ne ingancin bayyana karatun sallah ga mu mata? Shin akwai banbancin tsakanin sallar mace da namiji?

    𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

    Wa'alaikumus Salam warahmatullahi Wabarkatuh

    Malamai sun yi ijma’i a kan bayyana karatu a cikin dukkan raka’o’i biyu na sallar Asubah, da raka’o’i guda biyu na farkon sallar Maghriba, da raka’o’i guda biyu na farkon sallar Isha’i. Haka kuma da sirranta karatun a cikin dukkan raka’o’in sallar Azahar da La’asar da raka’ar karshe ta Maghrib da raka’o’i biyu na karshen Isha’i. (Aslus Sifah: 2/413)

    Sannan kuma ya tabbata a cikin Hadisin Maalik Bn Al-Huwairith (Radiyal Laahu Anhu) cewa Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:

    « ﻭَﺻَﻠُّﻮﺍ ﻛَﻤَﺎ ﺭَﺃَﻳْﺘُﻤُﻮﻧِﻰ ﺃُﺻَﻠِّﻰ »

    Kuma ku yi sallah kamar yadda kuka ganni ina yin sallar. (Sahih Al-Bukhaariy: 631)

    Wannan gamammiyar dokar ta haɗe maza da mata daga cikin musulmi, sai in an samu wurin da ya cire matan daga hakan.

    Al-Imaam Al-Mujaddid Al-Albaaniy a ƙarshen littafinsa: Sifatu Salaatin Nabiy (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya bayyana cewa: Babu wani abin da ya zo a cikin Sunnah da yake hukunta cire mata a cikin siffar Sallar Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam). Har kuma ya kawo maganar da Ibn Abi-shaibah ya riwaito da ingantaccen isnadi daga Ibraahim An-Nakha’iy (Rahimahul Laah) ya ce:

    ﺗَﻔْﻌَﻞُ ﺍﻟْﻤَﺮْﺃَﺓُ ﻓِﻲ ﺍﻟﺼَّﻠَﺎﺓُ ﻛَﻤَﺎ ﻳَﻔْﻌَﻞُ ﺍﻟﺮَّﺟُﻞُ

    Mace a cikin sallah tana aikata irin abin da namiji yake aikatawa ne. (Aslus-Sifah: 3/1040)

    Sannan kuma yana da kyau mu san cewa: Bayyana karatu ba yana nufin daga murya sai kowa da kowa a kusa da na nesa ya ji ba ne. Amma dai ɗagawa ne ta yadda mai sallah zai jiyar da kansa da wanda yake kusa da shi.

    Kuma maganar cewa wai muryar mace al’aura ce ba daidai ba ce, domin dai maganar Allaah Ta’aala ta warware ta inda yake cewa:

    يَا نِسَاءَ النَّبِيِّ لَسْتُنَّ كَأَحَدٍ مِنَ النِّسَاءِ ۚ إِنِ اتَّقَيْتُنَّ فَلَا تَخْضَعْنَ بِالْقَوْلِ فَيَطْمَعَ الَّذِي فِي قَلْبِهِ مَرَضٌ وَقُلْنَ قَوْلًا مَعْرُوفًا

    Yã mãtan Annabĩ! Ba ku zama kamar kõwa ba daga mãtã, idan kun yi taƙawa, sabõda haka, kada ku sassautar da magana, har wanda ke da cũta a cikin zuciyarsa ya yi ɗammani, kuma ku faɗi magana ta alheri. (Surah Al-Ahzaab: 32)

    Wace magana ce kuwa ta fi Alƙur’ani kyau da alheri?!

    Allaah ya fahimtar da mu.

    WALLAHU A'ALAM

    Sheikh Muhammad Abdullaah Asslafiy

    Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu. . .

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://whatsapp. com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www. facebook. com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

    https://t. me/TambayoyiDaAmsoshi

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.