Shin Mutum Zai Yi Wanka Idan Ya Kalli Abin Da Ya Tayar Masa Da Sha'awa

     TAMBAYA (41)

    Assalamu Alaekum warahmatullahi wabarakatuhu. Patan malam yana lpy, Dan Allah ina d tambaya

    Dan Allah idan mutun ya yi tunani ko ya yi karatun littatafae ko kuma ko ya kallali wani abun d yatayar masa da sha'awarsa, shin sae mutun ya yi wankan janaba kafin ya yi ibada ko kuma kawae tsarki mutun xaeyi?

    Sannan miyake wajabta wankan? Allah ya ba da daman amsa minmin

    AMSA

    Waalaikumus, Warahmatullahi, Wabarakatuhum

    Alhamdulillah

    Idan har silar karatun littafin ko kuma kallon sai maniyyi ya fita to ya zama dole mutum ya yi wankan janaba

    Amman idan ba abin da ya fita to ba za ki yi wankan ba

    Domin kuwa wankan yana wajabtuwane ga kowanne baligi namiji ne ko mace silar fitar maniyyi a mafarki ko a farke

    Abubuwan da ke wajabta wankan janaba sun hada da fitar maniyyi silar mafarki ko kuma sha'awa, zubar jinin haila ko kuma boyuwar kaciyar namiji a gaban mace duk waɗannan suna wajabta wankan janaba

    Rashin yin wankan sabawa umarnin Annabi SAW ne domin kuwa Mala'ikun rahama ba sa shiga gidan da mai janaba yake ciki har sai ya kasance cikin tsarki

    Haka kuma kallon abin da kan tada sha'awa ko kuma karanta littattafan da za su gayyato sha'awa suma duk haramun mutum yake aikatawa saboda fadin Allah SWT

    ( وَالَّذِينَ هُمْ لِفُرُوجِهِمْ حَافِظُونَ )

    المعارج (29) Al-Ma'aarij

    Da waɗanda suke, ga farjojinsu, mãsu tsarewa ne

    Wallahu ta'ala a'alam

    Amsawa:

    Usman Danliti Mato (Usmannoor_As-salafy)

    Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu. . .

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://whatsapp. com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www. facebook. com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

    https://t. me/TambayoyiDaAmsoshi

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.