Ya Nemi A Biyasa Sadakinsa Don ta ce Ya Saketa Saboda Baya Haihuwa?

    𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

    Assslam alaika Dr don Allah a taimakamin da amsar wannan tambaya koya halatta mutum ya ce matarsa ta biyasa sadakinsa domin ta nemi ya saketa don baya haihuwa ?

    𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

    Wa'alaikumus Salam warahmatullahi Wabarkatuh

    To ɗan uwa asali a shari'a anayin kul'ine ya yin da mace ta nemi mijinta ya rabu da ita ma'ana ya saketa batare da wani uzuri ba matukar mace ta nemi mijinta ya rabuda ita babu uzuri babu dalili, to yanada yan'cin da zaice a biyasa sadakinsa, domin yaje yakara wani auren wannan shi ne abin da shari'a ta ce

    Amma a wannan hali matar nan tanada uzuri saboda baya haihuwa kuma daga cikin manufofin aure a shari'a shi ne asamu hayayyafa to shikuma baya haihuwa, ita kuma taga bazata iya hakuri ta zauna ta ci gaba da rayuwa da mutumin da baya haihuwa ba saita nemi ya sawwake mata ta je ta yi aure to anan ba shida yan'cin da zaice saita biyasa sadakinsa domin kuwa ya riga ya cinye sadakinsa kuma ya ci moriyarta ya amfana da ita sannan kuma tanada uzuri a shari'a sannan ko'a sharia za a iya raba wannan auren saboda tanada uzuri, don haka ya sawwake mata shikuma ya nemi wadda za ta iya hakuri da zama da shi har lokacin da Allah zai ba sa lafiya

    Allah shi ne mafi sani

    Amsawa

    Dr Abdallah Gadon kaya

    Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

    https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.