'Yar Damisa (Kashi na 2)

    Alhaji Damisa:

    Ba za ta iya shiga jami'a da shi ba ne?

    Hajia Jummala:

    Ba dai a yadda yake ba. Amma idan na samu Kawun ta dake Jami'ar jihar nan zai iya sama mata

    Alhaji Damisa:

    A'al ba dai y'a ta ba. Ta bayan fage?! Inaa. Ina take Lau... (Ya kama kiranta ke nan aka kwankwasa kofar gidan tare da sallama. Suka juya baki daya suka dubi kofar)

    Hajia Jummala:

    A'ah, waye wannan da sanyi safiyar nan?

    Alhaji Damisa:

    Ban sani ba amma bari in duba in gani (ya daga murya) Alaikumus-salam (Ya tashi ya nufi kofar ya bud'e)

    Direban Kamfani:

    Yalla6ai barka da asuba (cikin ladabi da biyayya)

    Alhaji Damisa:

    Barka ka dai Liman mai ya faru?

    Direba:

    Yalla6ai sabon injin nan ne ya tsaya a ma'aikata tun jiya da daddare. Anyi anyi a gyara abin ya citura shi ne MD ya turo ni maza in zo in kirawo ka.

    Alhaji Damisa:

    Injiniyan kamfani bai zo ba ne mai yasa bai gyara ba?

    Direba:

    Yana nan tun da karfe biyar na asuba amma injin bai gyaru ba. Anyi iya kokarin da za a yi a tada shi ya k'i tashi.

    Alhaji Damisa:

    Tun yaushe Manajan Darekta ya zo Kamfani? Don me ya sa ba a bugo min waya ba?

    2>3


    'Yar Damisa - Gabatarwa

    From the Archive of:

    Malam Muhammad Tajajjini Tijjani
    Imel: mmtijjani@gmail.com
    Lambar Waya: +2348067062960

    ©2023 Tijjani M. M.


    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.