Auren Kanin Kaka

    𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

    As-Salaam Alaikum. 'Yan uwa biyu ne maza kuma ’yan-uba, sai ’yar da babbansu ya haifa tayi aure kuma ta haifi yarinya, shi ne wai wannan yarinyar take son auren kanin kakanta. Tambaya a nan ita ce: Wai auren ya halatta?

    𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

    Wa Alaikumus Salaam Wa Ramatul Laah

    A kan bayanin matan da suka haramta ta hanyar dangantaka ga abin da Allaah Tabaaraka Wa Ta’aala ya ce

    { حُرِّمَتْ عَلَيْكُمْ أُمَّهَاتُكُمْ وَبَنَاتُكُمْ وَأَخَوَاتُكُمْ وَعَمَّاتُكُمْ وَخَالَاتُكُمْ وَبَنَاتُ الْأَخِ وَبَنَاتُ الْأُخْتِ }

    An haramta muku auren uwayenku, da ’ya’yanku mata, da ’yan uwanku mata, da goggoninku, da innoninku da ’ya’ya mata na ’yan uwanku maza, da ’ya’ya mata na ’yan uwanku mata. (Surah An-Nisaa’: 23).

    Abin nufi da ’ya’yanku mata, in ji malamai: Duk macen da namiji yake matsayin mahaifi gare ta, kamar ’ya ko ’yar ’ya, ko ’yarta duk kuwa yadda suka yi ƙasa. Kuma wannan yar ko ta aure ne aka same ta, ko ba ta aure ba ne.

    Ƙanin kakanta shi ne ƙanin mahaifin mahaifiyarta. Wannan bai halatta ba lura da wannan ayar.

    Sannan kuma ƙaidar da malaman Fiqhu suka shimfiɗa ma a nan ita ce

    Haram ne namiji ya auri duk wata macen da yake da dangantaka na jini da ita, sai dai guda huɗu kawai

    1. ’Yar baffansa.

    2. ’Yar kawunsa.

    3. ’Yar goggonsa.

    4. ’Yar innarsa.

    (Sahih Fiqhis Sunnah: 3/72).

    WALLAHU A'ALAM

    Sheikh Muhammad Abdullaah Assalafiy

    Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://chat.whatsapp.com/BSA30hdZD7V3WSJF8WVwUj

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

    https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.