Hukuncin Sakin Mace Mai Juna Biyu

    𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

    Assalamu Alaikum Malam! Mutum ne ya saki Matarsa tana da juna biyu, To ya hukuncin wannan sakin?

    𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

    Wa'alaikumus Salam Warahmatullah Wabarkatuh.

    Mutumin da ya saki Matarsa tana da juna biyu Matsala biyu ce a taƙaice

    1. Matsala ta Farko:- shin saki ya yuwu ko bai yuwuba? Alal haƙiƙa saki ya yuwu, kuma saki a lokacin da mace take da juna biyu; saki ne wanda ya halatta duk da cewa a cikin malaman fiƙihu akwai masu cewa saki da juna biyu bai halatta ba suna ƙirgashi a cikin Adɗalaƙul bida'i.  Amma a cikin nafsin ƙur'ani za a fahimci cewa ya halatta, wanda wannan shi ne fatawar sauran malaman.

    Dalilin faɗin Allah maɗaukakin sarki: " Mata ma'abauta juna biyu iddarsu shi ne su haife a binda ke cikin cikinsu"

    To kaga da sakin bai halitta ba; da Allah ba zai shagalta wajen faɗin yadda za su yi idda ba, yadda Ubangiji ya tsaya ya yi sharhin yadda za suyi idda, wannan dalilin ne a kan cewa sakin ya yuwu, wannan dalilin ne kan cewa sakin ya halatta, to dan haka duk wadda aka saka da juna biyu sakin ya halatta kuma ya yuwu ( ta saku ).

    Yanzu abinda ya rage shi ne iddarta ba za ta fita daga ciki ba, har sai lokacin da ta haihu, ko yau aka saketa sai ta haihu gobe ko jibi, ka ga kwana biyu kenan to ta fita daga idda ya halatta tayi Aure.

    2. Sannan abu na gaba:- wajibi ne ga miji ( wanda ya sake ta ) ya zamanto ciyar da ita, shayar da ita, tufar da ita, duk suna a wuyansa gidan da za ta zauna ya biya haya, in gidan iyayen ta ne ciyarwa da shayarwa duk suna a wuyansa har lokacin da za ta haihu, idan ta haihu kuma dole ne ya ciyar da ita dan ta shayar da ɗansa, sai dai in ya samu wata mai shayarwa su kai ittufaƙin yadda zai biya, ya karɓe ɗan ya kai mata, saboda a shari'ance a kwai wannan, amma in ba haka ba shi zai riƙa ciyar da ita saboda shayar da ɗansa."

    WALLAHU A'ALAM

    ✍️ Abu Rukayya Falale

    Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://chat.whatsapp.com/IerSx3AH0ZSJyHIuIYfqds

    𝐅𝐀𝐂��𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

    https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.