Wakar Dan Tauri Basare Shanawa Ta Makada Kassu Zurmi Tare da Kirarin Dan Taurin

    Waƙar Ɗan Tauri Basare Shanawa, Shinkafi, Jihar Zamfara Ta Makaɗa Abubakar Amadu (Kassu Zurmi) Da Kirarin Ɗan Taurin( Basare). An ɗauki Waƙar a Gidan Rediyon Nijeriya na Kaduna a lokacin FESTAC 77 ( a cikin shekarar 1977)
    Daure Karen Gado kai nak kawo ni,
    Maganin maza na Jibo É—an Zaki, 
    Mahaukaci na Nabanga zulma,
    Nagode Marahwa É—an Zaki ka kyauta,
    Marahwa Iro ka nuna man iko,
    Uhnn! Haliku Allah ya baku arzukkkan Tswahhinku,
    Gagara dako Uban É—an Anna,
    Basaren gabas ga gulbin yamma Na Abdu,
    ÆŠan Isaka Na Nomau,
    Basare dutcin hwashin tama Na Jibo É—an Zaki,
    Katakoron Cibau Daudu,
    Na Abdu masu hwaÉ—an kashe kunya,
    Na Gajo ko daji ya ci su,
    Taro abin da dud É—aki yas samu,
    Sabad da dangarama yas same shi tun da dai ita nak kawo shi,
    Mutane abin É—aki baya samuwa banza,
    Basare ɗan Isaka sai ƙohwa ta buɗe,
    Yan Tauri ku riƙe ni gaskiyar Allah,
    Yanzu Kassu na zan matatc tcara,
    Aa' kaga muji baya son mu sai ran taron kunya,
    Sai wani taro ƙato ya yi ko kuma taron Daba,

    Kirari:
    Ar Kassu ar Kassu,
    KiÉ—i yakai ga babbak'u na bakin lamba,
    Anna waÉ—an da ba'a yada ma wuta,
    Aradu gahwara wuta salamu alekum,
    Kowak kwana lahiya shi yas so,
    Kanhwai nike mugun bance,
    Ƙaya nike babban ligido,
    Allobah hannu tamburan a sa maki É“awa,
    Makarin mugu bakin daji,
    Ni ak Kahiri Karen Nabanga zulma,
    Ni ak Karen Marahwa jikan Sambo,
    Kada in ƙara ji,
    Kada in ƙara gani,
    Ni ak Kahiri Karen Tudun Shanawa,
    Asakon dare sai mai Kura,
    Daidai mai Akuya ya É—amre,
    Zucciyam mutun birni nai,
    Yan Tauri kowa yasan kowa yan tcelen uwag ga, 

    Gagarabadan dama da hauni, 
    Basare na Abdu annan koran yaÆ™i, 
    A tcarci maza kau akwai ranas su, 
    Ranak ku sai wuta sai a tara, 
    In an yi gobara É—aki ya kama, 

    Kirari:
    Ar Kassu ni ak Kanhwai mugun bance, 
    Ƙaya nike babbal ligidama,
    Allobah hannu tamburan a sa maki É“awa, 
    Makarin mugu bakin daji, 
    Ni ba kama Æ™areri Uban É—an Anna, 
    KiÉ—i yakai ga babbak'u na bakin lamba,
    Anna waÉ—an da ba'a yada ma wuta,
    Ni ak Kahirin gabag ga gulbin yamma, 
    Ni ak Kahiri na yamma ga gulbin gabas Uban É—an Anna, 
    Ni ak Kahiri Uban Yakubu,
    Ni ak Kahiri Karen Tudun Shanawa, 
    Ni ak Kahiri na Cibau Daudu, 
    Asakon dare sai mai Kura,
    Daidai mai Akuya ya É—amre, 
    Zucciyam mutun birni nai, 
    Yan Tauri kowa ya yi mai hissai, 

    Anne bai sha KiÉ—inmu kan banza, 
    Basare duk abun da niyyi nuhi ya bani, 
    Nayi godiya ga Nabanga zulma, 
    Ya bani turamen lailai,
    Shi kau Marahwa É—an Zaki ya kyauta, 

    Kirari:
    Ar Kassu ni ak Kahiri Karen Sardauna gwamnati, 
    Ni ak Kahiri da yardar Allah, 
    Kowa Allah kawa hwaÉ—a bashi hwaÉ—a,
    In rana ta hita tahin hannu baya ruhin ta, 
    In hwaÉ—a ya É“aci sai wa da Ƙane, 
    Sai kau baran da yaj ji yag gani yash shaida, 
    Ni ba kama Æ™areri, 
    Ni ba zuwa gida É—ai É—ai, 
    Ni dawaya kora, 

    Jama'a kowash sha KiÉ—i abinai yab bai, 
    Latton Marahwa na bad' É—inkin swace, 
    Bani É—unko wando tunas, 
    Sai kaji an ce Marahwa É—an Zaki ya bani, 
    Jama'a dai Allah shi maida Danda ga turkenta, 
    Yara in hali yak kama, 
    Yan kallon wuri kuce min amin, 
    Wanda dub bai ce muna amin ba damanab bana na kashe shi, 

    Amin! Amin!! Amin!!! 

    Kirari:

    Yihuuuuuu!
    Ar Kassu ance babban likita ya dawo,
    Ina shirin cika shi da aiki,
    Ni ag gata dawaya kora Uban É—an Anna,
    Ni ak Kahiri Musulmin yaƙi,
    Ni ak Kahiri baran na Tabawa,
    Ni ak Kahiri Karen Nabanga zulma,
    Yan Tauri kowa yasan kowa,
    Hannu baka da tsoro,
    Maciji ba ayi ma zagi uban ÆŠan Mowa,

    Kassu albarkacin uban É—an Anna,
    Na Gajo duh hwadama tas sanni sabad dakai na Hassan da Husaini,
    Ina godiya waÉ—an Gatawa,
    Na koma godiya ga mutanen Turba,
    Mun zarce sai Isa sai mun dawo,

    Kirari:
    Ar Kassu ni an na Abdu gako luddan Sarki,
    Kowash sha dani ya ginsa,
    Asakon dare sai mai Kura,
    Daidai mai Akuya ya É—amre,
    Ni ah Faru ba'a hwaÉ—an sara ta,
    Yan Tauri kowa niw wa nawa,
    Koway yi man ya yi man uban É—an Anna,
    Ni ak Kahiri uban ÆŠanbuzu,
    Gabad da yamma an san gata,
    Ni ak Kahiri na Cibau Daudu,
    Ni ak Kahiri Karen Tudun Shanawa,
    Karen Magaji mai Shinkahi,
    Ni ak Kahiri na Malan Bello,

    Shi ma Magaji ya nuna man iko,
    Kassu ina godiya wurin Malan ÆŠangwaggo,
    Da Isah Rwahin daji,
    Dangizgo yaron na Tabawa,
    Mahaukaci na Jibo É—an Zaki,
    Basare É—an Isaka masu hwaÉ—an kashe kunya,
    Na Abdu ko daji ya ci su,
    Gagarabadan dama da hauni uban ÆŠan Twanka,
    Basare na Gajo kaci maras sa kunya,
    Dawo Karen Gado anna kai yaƙi,
    Tauri ba banzaaa ba,
    Ba banza ne ba yara kun ji KiÉ—in ansar rai,

    Kirari:
     Ar Kassu ar Kassu, 
    Kace bismillahi La'ilahu Illallahu, 
    Ba Sarki sai Allah, 
    Ba Mala'ika awaj Jibirila, 
    Allah saini, 
    Allah saini Kassuwag ga ta gobe kassuwam mata ce, 
    Daji ko yaci ni ba'a ce man hoho, 
    Sai dai in nazo gida ace man barka, 
    Ni ag gata dawaya kora uban ÆŠanbuzu, 
    Gabad da yamma an san gata, 
    Manya ban da cin amanab barwai, 
    Barwai ban da cin amanab Barwai,
    Yan Tauri ku yi biya kuji daÉ—i, 
    Akwai magani ga dattab'ayye, 
    Kowab bi ta dattijo baya kunya daji, 
    Radda duk' Æ™arhe yayyi man jak kama ina da jawabi ni da dattib'ayye, 
    Ni ak Kahiri Ƙanen Hura Yan Sanda, 
    Ni ak Kahiri Karen Barau na Sa'idu, 

    Ayyururrrrrrru! 
    Ayyyyihu!! 

    A tcarci maza kau akwai Æ™aton ranas su wata rana, 
    Basare Sarki baya son ku sai daji ya É“aci, 
    Kuwa salad dogo sai ya gama yace Alhandu, 
    Kuwa ba tawaye ba don gari ya É—ebe kewa, 
    Basare maganin maza na Hassan da Husaini, 

    Kirari :
    Ar Kassu Ar Kassu 
    Ni ak Kahiri Karen Magaji mai Shinkahi, 
    Mu ab babbak'u mataka lamba,
    Ni ak Kahiri Baturen yaƙi,
    Ni ak Kahiri Nasaran yaÆ™i, 
    Ni aj Jamul É“ata Æ™asa uban Yakubu, 
    Masu gari ku riÆ™e mu riÆ™on amanar Allah, 
    Nesa ta zaka kusa,
    Komi ku kaso kun samu,

    Na Katakare sai mai lura! 
    Na Katakare sai mai lura!! 

    Sai ran taron Daba, 
    ÆŠan Isaka na Nomau, 
    Basare zakkaa awon maza na Hassan da Husaini, 
    Na Abdu masu hwaÉ—an kashe kunya, 
    Katakoron Cibau Daudu, 
    Basare na Abdu kaci mazaizai daji, 
    Zakkaa awon maza uban É—an Anna, 
    Basare zakkaa awon maza uban É—an Anna, 
    Basare maganin maza na Hassan da Husaini, 
    Uhmmmm!

    Daga Taskar:
    Malam Ibrahim Muhammad Birnin Magaji
    ÆŠanmadamin Birnin Magaji
    Imel: birninbagaji4040@gmail.com
    Lambar Waya: 08149388452, 08027484815 

    www.amsoshi.com

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.