Auran Yar Karamar Yarinya

    𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

    Assalamu alaikum. Ina fatar Allah ya kara ma Mallam Ikhlasi. Ya halatta idan mutum ya auri mace karama wadda ba ta fara jini ba ya sadu da ita? Kokuwa rainonta zai yi?

    𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

    Wa a alaikumassalam,

    Malamai sun cimma daidaito game da halaccin aurar ‘yar karamar yarinya, saboda ayata huɗu a suratu Addalak ta bada labarin yadda karamar yarınya za ta yi idda

    وَاللَّائِي يَئِسْنَ مِنَ الْمَحِيضِ مِنْ نِسَائِكُمْ إِنِ ارْتَبْتُمْ فَعِدَّتُهُنَّ ثَلَاثَةُ أَشْهُرٍ وَاللَّائِي لَمْ يَحِضْنَ ۚ وَأُولَاتُ الْأَحْمَالِ أَجَلُهُنَّ أَنْ يَضَعْنَ حَمْلَهُنَّ ۚ وَمَنْ يَتَّقِ اللَّهَ يَجْعَلْ لَهُ مِنْ أَمْرِهِ يُسْرًا

    Kuma waɗanda suka yanke ɗammãni daga haila daga mãtanku, idan kun yi shakka, to, iddarsu watã uku ce da waɗanda ba su yi haila ba. Kuma ma´abũta cikinna ajalinsu, (shi ne) cewa su haifi cikinnansu. Kuma wanda ya bi Allah da taƙawa, ( Allah) zai sanya masa wani sauƙi daga al´amarinsa.

    Hakan sai ya nuna ingancin yi mata aure kafin ta balaga, sannan Annabi Sallallahu alaihi Wasallam ya auri nana Aisha tana ‘yar

    shekara shida.

    Malamai sun yi saɓani game da lokacin da za a fara saduwa da ita, bayan anyi auren, akwai waɗanda suka tafi akan cewa dole sai ta balaga za a mikata ga mijinta. Wasu malaman sun kayyade shi da shekara (9) saboda Annabi Sallallahu alaihi Wasallam ya tare da nana A’isha ne bayan ta kai shekaru tara.

    Zancen da yafi zama daidai shi ne : za a duba yanayin jikin

    yarinyar, in har za a iya jima’i da ita ba ta cutu ba, za a iya mikata ga mijinta, ko da shekarunta kaɗan ne, saboda mata suna bambanta wajan girman jiki gwargwadon wurin da suke rayuwa, da kuma irin abincin da suke ci, sannan sharia ba ta iyakance lokacin da ake fara jima’i da mace ba.

    Don neman karin bayani duba: AlMugni 27/77 da kuma Alminhaj na Nawawy 9/206.

    Allah ne mafi sani

    Dr.Jamil Yusuf Zarewa

    Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://chat.whatsapp.com/CQ9TMXMrWDx1y7sYye2znU

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.