Hukuncin Wanda Janaba Ya Sameshi A Lokacin Sanyi

    𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

    Assalamu alaikum warahamtullahi wabarkatuhu!! Da fatan Malam yana cikin koshin lafiya Allah yasa, Malam tambayata itace : Ni inada jin sanyi koda sanyi kaɗan akeyi to ni inaji sosai har wasu sukance wai banida lafiya to Malam nakan tashi da asuba lokacin sallah wani lokacin Sai in tashi inji nayi mafarki kuma har na fidda maniyyi to a lokacin sanyi Malam bazan iya yin wanka ba zan iya yin taimama inyi sallah Malam in yaso daga baya inyi wanka???. Wassalamu Alaikum. Malam.

    𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

    Wa alaikumus salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.

    Ya halasta ga mai janabah yayi taimama a Waɗannan yanayin

    1. idan har bai samu ruwan da zai yi wanka ba,  kuma babu alamar samun ruwan har gari ya kusa wayewa.

    2. Idan ya zamanto yana tsoron kamuwa da jinya, ko Qaruwar wata jinya ajikinsa idan har yayi amfani da ruwan sanyi, kuma gashi awajen da janabar ta sameshi babu ruwan dumi, kuma babu damar dafawa ko samowa ruwan dumin kafin wayewar gari.

    3. Idan ya zamanto yana da wata larurar da ba zata yiwu ya taɓa ruwa ba ( koda na zafi ne).

    4. Idan ya zamanto yana cikin tafiya atsakiyar daji, da ruwa awajensa amma idan har yayi wanka dashi, bazai samu wanda zaisha ba, kuma rashin ruwan shan zai iya zama barazana ga rayuwarsa.

    To amma kai tunda kasan kana da wannan larurar jin sanyin, mai zai hana ka rika tanadin ruwan zafi a plask ka ajiye a ɗakinka ko water heater ko gas cooker wanda zaka rika dafa ruwan dashi?.

    Domin hakika yin taimama bazai halatta gareka awannan halin ba,  mutukar dai akwai yiwuwar samun ruwan dumi a inda kake, ko dumamashi kafin fitowar rana.

    WALLAHU A'ALAM.

    Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇 https://chat.whatsapp.com/GcU1I5wjOB18K4PA6eURQQ

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

    https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.