Saukowar Allah Zuwa Saman Duniya A Karshen Dare

    𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

    Assalamu alaikum mallam kwanaki na ji wani malami yana  bayani akan saukan Allah saman farko a karshen dare ko wani rana don amsa rokon bayinsa, amma sai mutumin ya karyata hadisin, yana mai cewa wai kowace kasa lokutan su daban wasu sai gari ya waye agun su tukunna mu daren mu yake rabawa, to ta yaya za ace Allah na sauka sulusi na karshe, kodai yana sauka a kowace kasa ne, in ji shi, haka ya yi wasa da hankulan mutane har kusan zan ce ni ma na kusa fadawa, Allah Ya kiyaye.

    Ina neman ko mallam zai yi sharhi akan wannan zance, koda Allah zai sa zuciyata ta samu nutsuwa. Allah ya saka da Alkhairi.

    𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

    Wa alaikum salam, Matsalar da mutumin ya samu shi ne ya kwantanta Allah da bayinsa ne, shi yasa ya kasa fahimtar hadisin.

    Duk wanda ya yarda cewa Allah ba ya kama da komai, kuma babu abin da ya yi kama da shi, wannan zai sa ya fahimci SIffofin Allah da kyau, ya kuma yi imani da su ko da kuwa sun zarta tunaninsa.

    Har a tsakanin bayi ana samun fifiko a sIffofi  da saurin zartar da lamura, saurin Aljani ba daidai yake da saurin mutum ba, karfin Zaki ba ya daidai da karfin akuya, balle kuma tsakanin bayi da mahaliccinsu, wanda ba sa kamanceceniya  da shi ta kowacce fuska.

    Hadisin saukowar Allah zuwa saman duniya, hadisi ne ingantacce, mutawatiri, sama da sahabbai ashirin (20) suka rawaito shi daga Manzon tsira, duka manyan kundayan hadisi guda tara (9), sun ambaci hadisin daga sahabi Abuhurairah.

    Bisa abin da ya gabata ya wajaba kowanne Musulmi ya yarda cewa, Allah Yana saukowa a karshen kowanne dare saukowar da ta dace da mulkinsa da katafaren ikonsa,

    Irin wadannan siffofin wadanda suke nuna girman Allah da rashin kamanceceniyarsa da bayi, suna da yawa a cikin hadisai, a ranar Alkiyama Allah zai sanya sammai guda bakwai a dan'yatsansa guda ɗaya.

    Allah ne mafi sani.

    Dr. Jamilu Yusuf Zarewa

    Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

    https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.