Mijina Ya Bar Saduwa Dani Saboda Ina Bleaching

    𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

    As-Salaam Alaikum Wa Rahmatul Laah. Yanzu rabon da mijina ya kwanta da ni shekara guda da watannin uku kenan, wai saboda ina ‘bleaching’ kuma ina da ƙyasfi, wanda kuma ya ƙi nema mini magani. To shin akwai aure a tsakaninmu ko babu?

    𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

    Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul Laah Wa Barakaatuh.

    Ƙwarai kuwa, baiwar Allaah! Akwai aure a tsakaninku mana.

    Ai duk auren da aka ɗaura shi a bisa ƙaidoji da dokokin Musulunci ba ya mutuwa haka siddan sai in an kashe shi. Maana: Har sai in shi mijinki da kansa ya fito ƙarara ya ce ya sake ki, ko kuma sai in ke da kanki kin rabu da shi ta hanyar ba shi khuli, ko kuma idan magana ta kai gaban alƙali, kuma ya bincika sannan ya gano akwai cutarwa a tsakaninku ko a addini idan aka bar ku kuka cigaba da zama. Daga nan ne shi ma yana iya sanya ƙarfin matsayinsa ya kashe auren ya raba tsakaninku.

    Don haka, idan har kina ganin ba za ki iya haƙurin cigaba da zama da shi ba saboda wannan cutarwar, to Sharia ta ba ki daman ki kai maganar gaba: Da farko dai ga iyayensa, in kuma ba a samu biyan buƙata ba sai ga iyayenki. Idan sun kasa warware matsalar, to kina iya wucewa zuwa wurin alƙali, amma tare da izininsu. A nan ne shi alƙali zai yi cikakken bincike mai zurfi a kan matsalar kuma ya gano gaskiyar daawarki, daga nan kuma ya fitar miki da haƙƙinki.

    Kodayake ‘bleaching’ saɓon Allaah ne, amma kuma shari’a ba ta bai wa mijinki daman ya ƙaurace miki na tsawon shekara saboda kin yi wannan saɓon ba, haka kuma ko domin kina da ƙyasfi a fatar jikinki ba. Domin iyakan tsawon lokacin da Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ƙaurace wa iyalansa don ladabtarwa shi ne wata guda kaɗai. Amma har tsawon shekara, wannan abin da ya yi ya ci karo da maganar Allaah Maɗaukakin Sarki da ya ce

    يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا لَا يَحِلُّ لَكُمْ أَن تَرِثُوا النِّسَاءَ كَرْهًا وَلَا تَعْضُلُوهُنَّ لِتَذْهَبُوا بِبَعْضِ مَا آتَيْتُمُوهُنَّ إِلَّا أَن يَأْتِينَ بِفَاحِشَةٍ مُّبَيِّنَةٍ وَعَاشِرُوهُنَّ بِالْمَعْرُوفِ فَإِن كَرِهْتُمُوهُنَّ فَعَسَىٰ أَن تَكْرَهُوا شَيْئًا وَيَجْعَلَ اللَّهُ فِيهِ خَيْرًا كَثِيرًا  

    Ya Ku waɗanda suka yi ĩmãni! Bã ya halatta a gare ku, ku gãji mãtã a kan tĩlas kuma kadaku hana su aure dõmin ku tafi da sãshen abin da kuka ba su, fãce idan suka zo da wata alfãsha bayyananniya kuma ku yi zamantakwa da su da alhri sa'an nan idan kun ƙĩ su, to akwai tsammãnin ku ƙi wani abu alhãli kuwa Allah Ya sanya wani alhri mai yawa a cikinsa. (Surah An-Nisaa’: 19).

    Don haka, abin ya ke wajibi a kan mai irin wannan abin shi ne ya tuba ga Allaah Ubangijin Halittu kuma ya komo ga sauke haƙƙoƙinsa dangane da matar aurensa.

    WALLAHU A'ALAM

    Sheikh Muhammad Abdullaah Assalafiy

    Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.