Suratul Mulk Tana Tseratarwa Daga Azabar Kabari

    𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

    Suratul Mulk Tana Tseratarwa Daka Azabar Qabari, Shin Sau Nawa Akeson Karantata Sau Ɗaya Arana Ko Samada Ɗaya?

    𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

    الحمد لله.

    Daka Abu huraira Allah yakara masa yarda daka Annabi Sallallahu Alaihi wasallam ya ce: akwai wata sura acikin Alqur'ani tanada ayoyi talatin za ta ceci mutum harsai Angafarta masa itace (Tabarakallazi biyadihil Mulku) Turmuzi (2891) da Abu dauda (1400) da ibnu majah (3786).

    Shaikul Islam ibnu taimiyyah ya ingantashi acikin maj-mu'u fatawa nasa (22/277) da shaik Albani acikin sahihu ibnu majah (3053).

    Abunda ake nufi da wannan shi ne mutum yakarantata kowanne dare, yakuma yi aiki da abundake cikinta na hukunce-hukunce, yayi imani da abundake cikinta na larabai.

    Daka Abdullahi Ɗan Mas'ud Allah yakara masa yarda ya ce: Wanda yakaranta (Tabarakallazi biyadihil mulku kowanne dare, Allah zai hana masa Azabar kabari saboda ita, Mun kasance azamanin Annabi Sallallahu Alaihi wasallam muna kiranta da (Mani'ah) lallai acikin littafin Allah akwai wata surah mai ayoyi talatin wanda yakarantata kowanne dare madallah dashi kuma ladansa ya yawaita, Nisa'i (6/179) Albani ya ingantashi acikin Sahihu Targeeb wattar-heeb (1475).

    Malaman lajnatul da'imah sukace: Abisa wannan anasan duk wanda yai imani da wannan sura yakiyaye karantata, dan neman yardar Allah, da ɗaukar izina da abundake cikinta na wa'azozi da abubuwan lura, yai aiki da abundake cikinta danta ce-ceshi.

    Fatawa lajnatul da'imah (14/ 334-335).

    WALLAHU A'ALAM.

    Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

     https://t.me/TambayaDaAnsa

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.