Hukuncin Azumin Wanda Ya Fitar Da Maziyyi Da Gangan

    𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

    Assalamu alaikum da fatan Malam yana nan lfy. Ya iyali. Mallam inada tambaya? Mallam menene hukuncin azumin wadda ya fitar da maziyyi ta hanyar tunani ko kuma taɓa jikin mace.?

    𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

    Wa alaikumus salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.

    Wanda ya fitar da maziyyi da gangan ta hanyar taɓa jikin mace ko ta dalilin yawaita tunani akan abinda ya shafi jima'i, to tabbas azuminsa ya karye. Kuma zai rama azumi ɗaya ne amadadin wannan da ya karya ɗin. Wannan ita ce fatawar Mazhabin Imamuna Malik.

    Don Qarin bayani aduba litattafan fiqhun Malikiyyah kamar Muqaddimatul Iziyyah da Risalatul Qairawaniy.

    WALLAHU A'ALAM. 

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
    https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

     https://t.me/TambayaDaAnsa

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.