Hukuncin Wanda Yake Cikin Sallar Nafila Sai Aka Tayar Da Iqama

    𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

    As-Salaam Alaikum. Menene hukuncin wanda yake cikin nafila sai aka tayar da iqama? Zai dakatar ne ko kuwa zai iya kammalawa?

    𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

    Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul Laah.

    Akwai maganganun malamai mabambanta har guda tara (9) a kan wannan mas’alar, kamar yadda mai littafin Al-Bahrul Muheetut Thajjaj (15/250-252) ya kawo. 

    Amma maganar da ta fi ita ce wacce ta dace da maganar Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) da ya ce

    « إِذَا أُقِيمَتِ الصَّلَاةُ فَلَا صَلَاةَ إِلَّا الْمَكْتُوبَةُ »

    Idan aka tayar da iqama to babu wata sallah sai wannan ta farillar. (Sahih Muslim: 710).

    A nan kowace irin nafila ba ta halatta ba a lokacin da aka fara tayar da iƙama. Kuma da zaran an fara tayar da iƙamar shikenan nafilar ta warware, ba sai shi mai sallar ya warware ta ba.

    Akwai ayar da waɗansu malamai suka kafa hujja da ita a kan halatta cigaba da nafilar matuƙar dai ba zai rasa kabbara ko raka’ar farko ba, wato

    وَلَا تُبْطِلُوا أَعْمَالَكُمْ

    Kuma kar ku ɓata ayyukanku. (Surah Muhammad: 33).

    Malaman da suke da wancan ra’ayin sun amsa da cewa, a nan ai ba mai sallar shi da kansa ne ya ɓata nafilar ba. Shari’ar musulunci ce ta ɓata ta, kamar yadda nassin hadisin da ke sama ya nuna. Al-Bahrul Muheetut Thajjaj (15/253).

    Amma kamar yadda ya gabata, akwai waɗansu malaman da suka zaɓi cewa, matuƙar dai ba zai rasa kabbarar farko na sallar da aka tayar da iƙamarta ba, saboda ya riga ya yi nisa a cikin nafilar ko domin limamin yana daɗewa kafin ya yi kabbarar harama, to a nan suna ganin zai iya cigaba har ya kammala nafilar. (Al-Mausuu’atul Fiqhiyyah: 1/356, As-Sharhul Mumti’: 4/164).  

    WALLAHU A'ALAM

    Sheikh Muhammad Abdullaah Assalafiy

    Ga masu tambaya sai su turo ta WhatsApp number: 08021117734

    Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
    https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

     https://t.me/TambayaDaAnsa

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.