Yadda Ake Danbagalaje Da ‘Yartsame Da Kwalan

    Ɗan Bagalaje

    Kayan haɗin ɗanbagalaje:

    i. Alabo           

    ii. Albasa        

    iii. Attarugu   

     iv. Gishiri

    v. Manja         

    vi. Ruwa         

    vii. Tattasai

    Za a daka alabo ya yi laushi sannan a tankaɗe. Daga nan za a sanya ruwa a kwaɓa. A ciki za a yanka albasa da tattasai da attarugu sannan a sanya gishiri. A gefe guda kuma, za a aza kasko bisa wuta sannan a sanya manja. Za a riƙa zuba wannan kwaɓaɓɓen garin alabo sannu a hankali ana soyawa tamkar yadda ake suyar ƙosai. Ana cin ɗan bagalaje ne da yaji.

    ‘Yar Tsame

    Kayan haɗin ‘yartsame:

    i. Albasa         

     ii. Gero            

    iii. Kanwa

    iv. Mai             

    v. Ruwa

    Hanyar sarrafa ‘yar tsame daidai take da ta masar gero da aka yi bayani a ƙarƙashin 13.1 da ke baya. Bambancin kawai shi ne, ana soya masar gero ne a cikin tanda. Ita kuwa ‘yar tsame ana soya ta ne a cikin kasko tamkar ƙosai. Yawanci ‘yar tsame ba ta kai masa girma ba. Wannan ke ba ta dama ta soyu sosai a cikin mai fiye da masar geron.

    Ƙwalan

    Kayan haɗin ƙwalan:

    i. Alabo           

    ii. Albasa       

      iii. Attarugu    

    iv. Gishiri

    v. Manja ko man gyaɗa          

    vi. Ruwa         

    vii. Tattasai

    Yadda ake ƙwalan yana da matuƙar kama da yadda ake ɗan bagalaje (kamar yadda aka yi bayani a sama ƙarƙashin 13.1.4). Bambancin kawai shi ne, ana kwaɓa ƙullun ƙwalan ne ruwa-ruba ba kamar na ɗan bagalaje ba. Bayan haka, ana soya shi ne a tanda ko ƙaramin kasko tamkar yadda ake soya masa. Za a riƙa ɗiga mai kaɗan sannan a zuba ƙullun ɗan kaɗan. Yayin da ɓangare guda ya soyu, sai a juya zuwa ɗaya ɓangaren. Za a riƙa yi ana ɗiga mai kaɗan-ƙaɗan har ya yi yadda ake so. Ana cin ƙwalan da yajin borkono.

    The book “Cimakar Bahaushe” (Diets of the Hausa People) is a collection of 293 traditional and modern diets of the Hausa people. Detailed explanations of the recipes and ingredients are provided. Comments are provided on the areas of the Hausa land where specific diets are mostly found, the age categories of people that usually use it, as well as the scientific impact of some of the diets to human biology.  Data is collected from interviews with different categories of people including:  i.                    Food sellers within the Hausa land: Mainly to have an idea of recipes on the diets.  ii.                  People of older age: Mainly to have insights on traditional diets of the Hausas.  iii.               Hausa scholars: Mainly to verify and justify the validity of the information obtained as well as provide further expert explanations on the diets.  Moreover, over two hundred (200) pieces of literature were reviewed to have better insight on the topic in question as well as get scientific and professional clarifications on some key concepts relevant to the research. The pieces of literature cover major relevant phenomena such as diet and hunger. Others are on the Hausa land and the Hausas.  The book contains thirty-three (33) chapters. Chapter one is the main introduction in which a concise explanation is provided on the Hausas, their history, their land, social life, and transformations due to globalization, acculturation, and modernity. Chapter two detailly discusses the concepts of diet and food from the Hausa point of view. That includes the meaning and the usage of diets in some Hausa works of literature both verbal and written (i.e. prose, poetry, proverbs, etc.).  Chapters three and four discuss the sources of Hausa diets and their forms accordingly. Chapters five to seventeen discuss some traditional Hausa diets including hard and soft ones. Chapter eighteen concentrates on the influence of modernity and globalization on Hausa diets. It has been discovered that there have been some significant changes in the Hausa diets ranging from recipes to kitchenettes.  Chapters nineteen to thirty-two discuss modern Hausa diets. Some traditional diets are still retained with little modifications, while on the other hand, there are a lot of new ones. Chapter thirty-three discusses “hunger” from the Hausa point of view. The relationship between hunger and food is examined. Additionally, the use of hunger in various Hausa literary works is studied. It is concluded that hunger is like a disease whereby its cure is food.  7th November 2022
    Citation (Manazartar Littafin): Sani, A-U. & Umar, H.A. (2022). Cimakar Hausawa. Kano: WT Press. ISBN: 978-978-984-562-9.

    Get a copy:
    To obtain a copy of this book, kindly send a WhatsApp message to:
    +2348133529736

    You can also write an email to:

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.