Shin Dole Sai Liman Ya Saka Hula Idan Zai Ja Sallah

    TAMBAYA (114)

    Aslkm. Allah ya gafata Malam! Akwai wani masallaci a unguwar mu limamin yana korar mutane idan suka shigo sahun gaba sbd Basu da HULA akan su. Dan Allah inaso a gayamin inda akace idan mutum bashi da hula akan sa bazai shiga sahun gaba ba ko Kuma bazai Yi limanci. Da wace hujja ya dogara. Nagode. Dan Allah taimaka a amsa min

    AMSA

    Waalaikumussalam, Warahmatullahi, Wabarakatuh

    Alhamdulillah

    Kamata yayi ku da kanku ku je ku same shi, ku tambayeshi cikin siyasa da girmamawa, Baba a ina ka samo dalili akan dole sai da hula a kai sannan mutum zai shiga sahun gaba? Farillah ne ko Sunnah ce, ko kuma Mustahabbi ne?

    Alal haqiqa, babu wani nassi da ya tabbata cewar dole sai da hula sannan sallah zata amsu

    Ya manta da hadisin da Annabi (Sallallahu alaihi wasallam) ya ce: "Allah ba ya duba izuwa ga surorinku da dukiyoyinku saidai yana duba ne izuwa ga ayyukanku da zuciyoyinku"

    (Sahih Muslim)

    Saidai, yana da kyau mutum ya yi shigar kamala idan zai gana da Ubangijinsa ta hanyar saka sutura mai kyau saboda hadisin: "Innallaha jamilun, yuhibbul jamal" ma'ana "Allah kyakkyawane kuma yana son abu mai kyau"

    (Sahihul Bukhari)

    A iya dan karamin ilimi na bansan cewar yana daga cikin karbuwar sallah ace dole sai mutum ya saka tagiya (hula) ba

    Wallahu ta'ala a'alam

    Amsawa

    Usman Danliti Mato (Usmannoor_Assalafy)

    Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
    https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

     https://t.me/TambayaDaAnsa

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.