Fassarar Mafarkin Shugabanni

    TAMBAYA (127)

    Assalamualaikum .Mutun ne ya ke ta mafarki da shuwagabin Nigeria,tun daga alhaji shehu shagari har zuwa Bola Ahmed Tinubu cewa gashi ya zauna tare da kowane dayan su alokacin shi cikin walwala da anashuwa.Gafarta malam meke fasarar wannan mafarki ?

    ✍️AMSA A TAQAICE

    (Mafarkin shugabanni yana nuna nasara da kuma albishir na alkhairi)

    AMSA

    Waalaikumussalam, Warahmatullahi, Wabarakatuh

    Alhamdulillah

    To dan uwa, mafarkin ganin, shugabanni, dattawa, manya, masu fada aji, masu tunani, malamai dukkan fassarar wadannan yana nuna nasara da kuma albishir na alkhairi kamar yanda Tabi'i Muhammad Ibn Seerin (Rahimahullah) yayi bayani a cikin littafinsa na "Qamus din fassarar mafarki"

    SHARHI

    Sanin kanmu ne cewar shi mulki siffar Allah ne. Yana bada mulki ga wanda Ya so kuma a lokacin da Ya so. Shine ya bawa Fir'auna mulkin Misra (Egypt) don ya jarraba shi kamar yanda ya bawa Annabi Sulaiman (Alaihis Salam) mulkin duniya don ya jarrabashi. Na farko ya samu damar mulkar gari guda daya tak saidai bai tafiyar da mulkin yanda Allah yake so ba, shi kuma na biyu ya samu damar mulkar duniya gaba daya amman hakan bai rude shi ba, yayi mulkin adalci yanda Allah Yake so

    Kenan mafarkin shugabanni mabanbanta kuma an zauna dasu zaman walwala da annashuwa yanada alaqa da wanda yayi mafarkin

    Masu zagin shugabanni basa irin wannan mafarkin la'akari da kullum suna kwantawa ne da bakin cikin shugabancin da ake musu sabanin shi kuma wanda yake addu'a gare su da nema musu yafiyar mahaliccinsu kullum kokari yake ya ga an yada alkhairinsu komai kankantarsa da kuma boye sharrinsu komai girmansa

    Haquri akan halayen shugabannin da kuma tawakkali ga Allah akan zama a Nigeria ba komai bane face jarabawa daga Allah wannan dabi'a ce da take bayyana musamman ga dattawa nagari

    Don haka wanda yake irin wadannan mafarkan sai ya ci gaba da riqo da addininsa da koyi da sunnar wanda yazo da addinin da kuma ci gaba da yin addu'a ga shugabanninsa don samun kubuta daga halin da mutane suka tsinci kansu na zagi da aibanta shugabanni

    Ya Allah ka shirya mu ka rabamu da fasiqanci (zagin musulmi) domin kuwa daga cikinmu ai ake samun shugabannin

    Wallahu ta'ala a'alam

    Subhanakallahumma wabi hamdika ash-hadu anla'ilaha illa anta astaghfiruka wa'atubi ilayk

    Amsawa

    Usman Danliti Mato (Usmannoor_Assalafy)

    Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.