𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
السلام
عليكم
Malam mene ne hukuncin mutumin da ya kashe kansa sakamakon ya shiga kunci? Kuma menene matsayin masu yi masa addu'ar Allah ya jiqan sa, Shin hakan ya halasta ne ko kuwa? Ina son a yi min qarin bayani na gode.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
وعليكم
السلام
Mutumin da ya kashe kansa ya aikata babban zunubi daga cikin
manyan zunubai da malamai ke kira Kabá'iruz Zhunuub. Babu wani dalili da zai sa
mutum ya kashe kansa a yi masa uzuri a nan duniya, kuma Allah ya ce
...وَلَا
تَقْتُلُوا أَنفُسَكُمْ إِنَّ اللَّهَ كَانَ بِكُمْ رَحِيمًا
"kada ku kashe kawunanku, lallai Allah ya kasance mai
jinqai ne a gare ku". (Suratun Nisá'i, aya ta 29)
Hadisi ya tabbata daga Annabi (Sallallahu alaihi Wasallam)
cewa: "Duk wanda ya kashe kansa da wani abu, za a dinga yi masa azaba da
wannan abun a ranar Alqiyama" Duba Sahihu Muslim hadisi mai lamba 110.
Sai dai a aqidarmu ta Ahlussunnah waljamá'ah, duk wani saɓon Allah da mutum ya yi
Allah zai iya yafe masa idan ya so in banda shirka, kamar yadda aya ta 48 da ke
Suratun Nisá'i ta tabbatar
إِنَّ
اللَّهَ لَا يَغْفِرُ أَن يُشْرَكَ بِهِ وَيَغْفِرُ مَا دُونَ ذَٰلِكَ لِمَن يَشَاءُ
وَمَن يُشْرِكْ بِاللَّهِ فَقَدِ افْتَرَىٰ إِثْمًا عَظِيمًا
Lalle ne, Allah ba Ya gãfarta a yi shirki game da Shi, kuma
Yana gãfarta abin da yake bãyan wannan ga wanda Yake so, kuma wanda ya yi
shirki da Allah, to, lalle ne ya ƙirƙiri zunubi mai girma. (Suratun Nisá'i Aya ta 48)
Wannan ya nuna kenan Allah zai iya gafarta ma wanda ya kashe
kansa idan ya ga dama, idan kuma ya ga dama zai yi masa azaba, daga bisani a
fitar da shi daga azaba zuwa rahama matuqar ya mutu a kan musulunci, saboda
wanda ya kashe kansa ba kafiri ba ne. Allah ya tsare mu da mugun ji da mugun
gani. A taqaice dai lamarinsa na wurin Allah Ta'ala.
Haka nan kuma, game da yi ma wanda ya kashe kansa addu'a,
wannan shi ma ya halasta, matuqar ya kashe kansa a halin zamowarsa Musulmi.
Allah ne mafi sani.
Jamilu Ibrahim Sarki, Zaria.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
No comments:
Post a Comment
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.