Hadisin Da Aka Fara Rawaitowa

    TAMBAYA (146)

    Wanne Hadisi ne farkon rawaito wa ?

    AMSA

    An rawaito hadisi na farko ne a lokacinda Annabi SAW yayi HIJIRA daga MAKKA zuwa MADINA, bayan taguwarsa ta saukeshi a gidan ABU AYUBAL ANSARI RTA, ya sauka a BANI UNAIF, kudu maso yamma daga inda QUBA take, anan yafara kwana

    KULSUMU ibn HIDMI RTA shine wanda ya bashi dakin dazai kwana, sai SAADU ibn HAISAMA RTA shikuma sai yace ya RASULULLAH naga baki sunata zuwa wajenka amman babu gurinda zaka karbesu amman ga filina inda muke shanya dabino zamuzo musakamaka ZANA saika dinga karbar bakinka a wajen, a lokacinne akazo ana maraba da saukarsa

    Ananne wasu daga cikin mutanen garin sukace bari suje tsegumi da ganin kwakwaf, irinsu Abdullahi Ibn Salami, yana kallon fuskar ANNABI SAW yace kai wannan ba sauran qarin bayani ba maqaryaci baneba, bayan anyi tsit sai Manzon Allah SAW yace, AYYUHANNASU, AKSHUS SALAMA, WA'A INA DA'AMA, WASULUL ARHAMA, WASALLU BILLAYYA WANNASU MIYAMU TADKULU JANNATA BISALAMI

    Ma'ana; Yaku mutane ku yada aminci (sallama), duk inda zakuje, ba tsugudidi, ba munafurci, ba algungumanci, ba annamimanci, hadin fada, ba yi da mutane, duk abinda zaisa qauna shi zakuyi

    Sannan ku ciyarda mutane, kuyita abinci, ku sada zumunci, sannan kuyi sallah cikin dare zaku samu ALJANNAH ba wahala

    Sunan al-Tirmidhī 2485

    To amman yanzun anzo wani zamani wanda ba'a damu da yada sallamaba, ga munafunci yayi qatutu a zuciyoyinmu, sannan masu hali basa ciyarwa kowa sai rowa, gashi ba'a zumunci saikanada abin hannu, sannan sallarma anfi fifita neman duniya akanta, to ahakan zamu shiga ALJANNAH ?

    Wallahu ta'ala a'alam

    Subhanakallahumma wabi hamdika ash hadu an la ilaha illa anta astaghfiruka wa'a'tubu ilayka

    Amsawa

    Usman Danliti Mato, (Usmannoor_As-salafy)

    Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Questions and Answers

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.