LGBTQ - Auren Jinsi (Lesbianism Da Homosexuality) Sun Zamo Ruwan Dare

    TAMBAYA (39)

    Dan Allah inaso a taimaka a yi write up mai dumi a kan mata masu neman yan uwasu mata wllh kazantar ta yi yawa takai har basajin kunyar bayyana kansu a cikin jamaa. MENE NE hukuncinsu (Daga: Abu Said BUK)

    AMSA

    Innalillahi wainna ilaihirrajiun

    Na dade da fitar da amsar tambayar nan. Sai naga dacewar bari na sake dawo da rubutun laakari da mummunan halin da GWAMNATIN kasarmu ta Nigeria take ƘOƘARIN jefa mu ciki na karban YARJEJENIYAR SAMOA da take da alaƘa da kungiyar LGBTQ wato auren JINSI. Wal iyazubuillah. Muna cikin MUSIBA sai Kuma ga wata MUSIBAR da ta zarce wadda muke a baya. Wannan alamu ne na tashin ALƘIYAMA suke ta sake bayyana akan idanunmu da kunnuwanmu

    Rashin kunyar bayyana kansu a cikin jama'a yanada nasaba da raguwar imaninsu, kuma daman ya tabbata a hadisin Abu Hurairah RA yace ma'aiki SAW yace mutumin da yake aikata zina ana a cire masa imaninsa ne, imanin zai dinga yawo a saman kansa kamar hadari, bayan ya gama zinar sai imaninnasa ya dawo jikinsa (Abu Dawud da al-Hakim suka rawaitoshi, Shaikh Albani ya ingantashi a cikin Silsila Ahadis-Assahiha mai lambata 509)

    Lesbianism ga mata wadda ake kira da madigo da hausa basada banbanci da Homosexuality ga maza wato Luwadi halayyar wasu daga cikin mutanen Annabi Lud AS, jinsi ne kawai ya banbantasu amman sun kasance daga cikin manyan alkaba'ir wadanda kan iya zama silar salwantar imanin mai aikatawa idan bai tuba ba, a karshe a tashi mutum cikin al'ummar Annabi Lud AS wadanda Allah ya hallakar

    A binciken da nayi kwanannan naga wasu Archeologist (masana tarihin ragowar kasa da abinda ta kunsa tun zamanin da) sun gano wani gunki mai suffar mace a garin da aka halakar da mutanen Annabi Lud AS (Ana kiran wajen da "Dead Sea" wanda yake a kasar Jordan) da sukayi bincike sai sukaga gunkin macen ya dace da abinda ya faru a yankin shekaru dubunnai da suka gabata (Wallahu a'alam)

    Allah SWT ya sanardamu irin zunubin da mutanen Annabi Lud AS suke aikatawa na neman jinsi a cikin Suratul A'araf ayata 80

    "Da Luɗu, a lõkacin daya ce wa mutanensa: "Shin, kuna je wa alfasha, babu kõwa da ya gabace ku da ita daga halittu?"

    81) "Lalle ne ku, haƙiƙa kuna je wa maza da sha'awa, baicin mata; A'a, ku mutane ne maɓarnata."

    82) "Kuma babu abin da ya kasance jawabin mutanensa, face ɗai suka ce: "Ku fitar da su daga alƙaryarku: lalle ne su, wasumutane ne masu da'awar tsarki!"

    83) "Sai Muka tsirar da shi, shi da iyalansa, face matarsa, ta kasance daga masu wanzuwa"

    84) "Kuma Muka yi ruwa a kansu da wani irin ruwa; Sai ka duba yadda aƙibar masu laifi ta kasance!"

    Haka kuma bayanin hallakar da tsohuwar (wato matar Annabi Lud AS) da kuma mutanensa yazo a cikin Suratu Ash-Shu'araa daga ayata 165 har zuwa ayata 175

    165) "Shin kuna je wa maza daga cikin talikai?"

    (Yana nufin kuna luwadi ?)

    166) "Kuma kuna barin abin da Ubangijinku Ya halitta muku daga matanku? A'a, ku mutane ne masu ƙetarewa!"

    167) Suka ce: "Lalle ne haƙiƙa idan ba ka hanu ba, ya Luɗu! Tilas ne kana kasancewa daga waɗanda ake fitarwa (daga gari)."

    (Ya zama tilas ga kowanne musulmi yayi hani kuma ya Ƙyamaci wannan ta'asa ta auren jinsi kamar yanda Annabi Lud AS ya Ƙi sa)

    168) Ya ce: "Lalle ne ga aikinku, haƙiƙa, ina daga masu ƙinsa."

    169) "Ya Ubangijina! Ka tsirar da ni da iyalina daga abin da suke aikatawa."

    170) Sabõda haka Muka tsirar da shi, Shi da mutanensa gaba ɗaya

    ( إِلَّا عَجُوزًا فِي الْغَابِرِينَ )

    171) Face wata tsõhuwa a cikin masu wanzuwa

    (Wannan tsohuwar itace matar Annabi Lud AS, wadda masu bincike suka gano gawarta a suffar dutse wanda ke daukeda sinadarin gishiri a kasar Jordan. Wallahu a'alam)

    172) Sa'an nan kuma Muka darkake wasu

    173) Kuma Muka yi ruwan sama a kansu ruwa, sai dai ruwan waɗanda ake yi wa gargaɗi ya munana

    174) Lalle ne ga wannan, akwai aya, kuma mafi yawansu ba su kasance masu imani ba

    (To ammanfa dukda haka idan sun tuba Allah mai Jin Kai Ne ga bayinSa kamar yanda ya rufe labarin da:)

    ( وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ )

    175) Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙiƙa, Shi ne Mabuwayi, Mai jin ƙai

    Hakama a cikin addinin Judeo-Christian (Juda/Nasara) an haramta wannan babban laifi a cikin littafin Genesis Surah ta 19 ayata 4 zuwa 11, a cikin labarin Sodom da Gomorrah (mutanen Annabi Lud AS) sannan kuma Clement na Alexandria da Novatian ya kawo Ƙwararan hujjojin haramcin madigo da luwadi inda yace yana cikin al'adun yahudawa Ƙyamatar wasu dabbobi kamar irinsu zomo da weasel saboda nuna wasu sababbin dabi'u yayin jima'insu (ma'ana suna auren jinsinsu) to indai yahudawa zasu Ƙyamaci dabba silar wannan mummunar dabi'a ta auren jinsi ai mu musulmai ne mukafi cancanta mu tsani wannan kazamar dabi'a (Karin bayani yana cikin littafin "World Of Homosexuality" ma'ana "Duniyar Yan Luwadi" babin "Addini da Luwadi" shafi na 39, wallafar shahararriyar Marubuciyar India, Shekuntala Devi)

    Zanso mutane su karanta daya littafin nata mai suna "World of Lesbianism" ma'ana "Duniyar Yan Madigo"

    Wasu sun maida abin sana'a wadda da ita suke ci suke sha harma su dinka sutura. Yayin da wasu kuma shaidan ya Ƙawata musu laifin a matsayin dabi'a, Ƙwalamar son abin duniya da kuma rashin kiyaye al'aura ke sa shaidan ya Ƙawata musu zunubin a matsayin dabi'a wadda yana wahala kaga mutum ya tuba, sai fa wanda Allah SWT ya tseratar. Haka kuma yawan kallace-kallacen fina-finai yana taka muhimmiyar rawa wajen fadawa tarkon zina, madugo da luwadi domin kuwa wasu abubuwan mostly anan ake koyonsu. Addu'ar da Ma'aiki SAW ya roƘa ta kada Allah ya halakarda al'ummarsa  kamar yanda ya halakar da na baya itace dalilin da yasa har yanzu Allah bai sa an halakar damu ba dukda cewar laifuffukan da mukeyi ma sun shafe na al'ummar da suka gabacemu

    Gashi mun tsinci kanmu a wani zamani na hauhawar farashin komai da komai, to wannan jarabawace kamar yanda Allah SWT ya fada a cikin Suratul Mulk ayata 2, kuma idan mutum ya ci test din ya kiyaye hannunsa daga sata silar talauci, ya kiyaye abinda ke tsakanin cinyoyinsa (farjinsa kamar yanda Allah ya fada a cikin Suratul Mu'uminun ayata 5) dakuma abinda ke tsakanin lebbansa (wato harshensa, Mu'uminun ayata 3) to Allah yana masa albishir da Aljannah (Mu'uminun ayata 10 zuwa 11) idan kuma masu kudi sukai amfanida kudinsu wajen lalata mata da maza ta hanyar sakasu a wadancan kazaman hanyoyi to saidai muce "Inna rabbaka labir mirsad" maana "Allah yananan a madakata" yana jiran kowa. Zabi ya rage namu

    Rashin ambaton Allah shine dalilin dayasa muketa kidimewa, yanzu dai ka duba kaga mutane duk sun daga hankali akan tashin farashin petrol, to idan Dajjal ya bayyana wanne halin rikici za'a kasance kenan, kaga ai sai wanda Allah ya tserar kawai. Kuma daga cikin yawan wadanda zasu bi Dajjal a karon farko sune yahudawan Kasar IRAN su 70,000 sannan kuma sai mata dayawa da kuma yayan da aka haifa ta hanyar zina wanda kuma ya tabbata a cikin hadisin Abi Umamah Al-Bahili RA yace: Ma'aiki SAW yace: "An nunamin a cikin mafarki na ana yiwa wasu maza da mata azaba a cikin wani kwatami mai tsananin doyi, da na tambaya sai akacemin ai wannan mazinata ne" (Ibn Khuzaima lambata 1986 da Ibn Hibban da wasunsu sannan Nasiruddin Albani ya ingantashi a cikin Sahihut Targhib lambata 991)

    A kula: Wannan fa makomar mazinata kenan wadanda basu tuba ba, ina kuma ga makomar masu luwadi da madigo ?

    Akwai hadisin Ibn Abbas Radiyallahu anhu, yace Maaiki Sallallahu alaihi wasallam yace: "Ku kashe Wanda ya aikata aiki irin na mutanen Annabi Lut da Kuma Wanda aka yiwa aikin"

    Al-Tirmidhi (1456), Abu Dawud (4462) da kuma Ibn Majah (2561)

    Al-Albany ya hassanashi a cikin Sahih al-Tirmidhi

    Ga kuma daya hadisin na Ibn Abbas, Maaiki Sallallahu alaihi wasallam yace

    "Ya Allah ka laanci Wanda ya aikata aiki irin na mutanen Annabi Lut" Sau 3 Yana tsine musu

    Hadisin yana cikin Musnad na Imam Ahmad mai lambata 2915

    Shu'aib al-Arna'ut ya hassanashi a cikin TahƘiƘ al-Musnad

    Nidai kam lamarinnan abun tsoro ne ga wanda yasan girman zunubbin

    A shawarce ina son nayi amfanida wannan damar wajen janyo hankalin iyayenmu da kuma malamai akan su daina amfanida littafin "Ƙueen Primer" Part II wajen koyar da yayansu na Nursery da Primary domin kuwa manufar mawallafan wannan littafin (Nelson Publishers Limited) shine su koyawa yayanmu musulmai aƘidar auren jinsi (Homosexuality, Lesbianism da ake kirada LGBTQ). A shafi na 5 cikin littafin sun rubuta "Let us be gay. Let us run" ma'ana "Mu zamo gay. Mu gudu". Sai kuma shafi na 22 inda suka rubuta "Is this the way. Yes, let us be gay" ma'ana "Wannan ce hanyar. Eh, mu zamo gay" (Wal'iyazubillah). Silar hakan tuni gwamnatin jihar kano ta umarci malaman Nursery da Primary da su gaggauta dakatarda amfani da irin wannan littafin da makamantanshi wajen koyarda yayanmu yaren English

    Hakama a hanasu kallace-kallacen Tom & Jerry domin kuwa akwai bincike mai zaman kansa da nayi wanda babu lokacin fayyaceshi anan. Sannan kuma a hana yara amfanida Games irinsu Subway Surfers wadda itama a hankali a hankali sun fara bayyana manufarsu ta auren jinsi ta hanyar updating game din da wata sabuwar fuska mai suna "Rain" yar jihar New York dake Amurka mai sanye da kaya launukan bakan gizo (Rainbow) wanda daman shine alamar masu aƘidar auren jinsi (LGBTQ). Na bibiyi posting dinsu inda sukace "Subway Surfers da hadin gwiwar LGBTQ da kungiyar taimakon marayu na muku maraba da sabon tsarinsu". Sun saka kungiyar taimakon marayune saboda yawancin marayu sunada naƘasu da kuma neman taimako na gaggawa musamman idan akwai Ƙarancin fahimtar addini a taredasu. Kumadai munsan yanda wannan Game ta Subway Surfers ta samu karbuwa sosai. Saidai muce Allah ya tsare mana imaninmu baki daya

    A karshe ina mai bawa kaina shawara da kuma masu karanta wannan sako da ma sauran musulmi baki daya, da mu yawaita istighfari, sannan mu yawaita halartar karatuttukan addini ko don samun bonanzan taka fuka-fukan mala'ikun rahama, zanso mu nemi littafin "Adabul Mufrad" wallafar Imam Al-Bukhari, mu karanta littafin "Talbis Iblis" wallafar Ibn Al-Ƙayyim dalibin Ibn Taimiyya, a littafin zakagane yanda Iblis yake danawa musulmai tarko, kai har malamai ma bai barsu a bayaba

    Sannan mu karanta littafin "Zaadul Ma'ad" wato "Guzurin AlƘiyama" na Ibn Al-Ƙayyim" domin kuwa ko sanda aka sakani makarantar boarding saida aka hadani da Provision (Guzuri) ballantana kuma zuwa Lahira, tabbas ita yakamata a hadawa guzuri tunda zuwanta ya zama dole

    Ya Allah duk wanda yake da HANNU akan wannan doka ta LGBTQ ka maida bala'in a Kansa, ka kiyayemu ka tsare Imaninmu

    Ku tayamu yada wannan saƘo, Allah kadai yasan adadin mutanen da zaka zama silar shiriyarsu

    Amsawa

    Usman Danliti Mato, (Usmannoor_As-salafy)

    Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Questions and Answers

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.