Wasu Hadisan Manzon Allah (SAW) Da Aka Rubuta Domin Gaisuwar Juma'a

    Waɗannan wasu hadisan Manzon Allah (SAW) ne waɗanda aka tsara a kan hotuna na musamman domin turawa a matsayin gaisuwar Juma'a. Wannan hanya ce babba ta tunasar da 'yan uwa da abokan arziki.
    Hadisi
    Juma@t Mubarak🕊️⛈️

    Duk lokacin da Manzon Allah (SAW) ya ga za a yi ruwan sama, yakan ce: "ALLAHUMMA SAYYIBAN NAFI-AN" 
    Ma'ana: "Ya Allah ka ba mu ruwa mai albarka.” (Sahih Al-Bukhari: 1032, Littafi: Book 15, Hadith 27)

    Hadisi
    Barka da Juma'a🕊️

    Manzon Allah (SAW) ya ce: "Mutane za su kasance kamar fari, masu ƙarfi suna cin masu rauni (babu tausayi), har dai ƙiyama ta tsaya a kansu." (Silsilatus Sahiha: 1953)
    Hadisi
    Manzon Allah (SAW) ya ce: "Lallai ne idan aka jinkirta maka mutuwa, sai kuma ka samu yin aikin ƙwarai domin Allah, to za ka samu ƙarin ɗaukaka. (Sahih Abi Dawud: 2864)
    Hadisi

    Manzon Allah (SAW) ya ce: "Lallai ne ita sa'a (ƙarshen duniya) ba za ta tsaya ba har sai an daina rabon gado (na dukiyar matattu) tukun. (Sahuh Muslim: 2899)
    Hadisi
    Manzon Allah (SAW) ya ce: "Da dai kun san ladar da kuke samu a wajen Allah a dalilin damuwa, da kuwa kun so a ƙara muku damuwa da talauci." (Silsilatus Sahiha: 2169)
    Hadisi
    Amru Ibn Hazmin Al-Ansari ya ce: "Manzon Allah (SAW) ya gan ni na jingina da wani ƙabari, sai ya ce:" "Kada ka cutar da mai ƙabarin."" (Silsilatus Sahiha: 2960)
    Hadisi
    Manzon Allah (SAW) ya ce: "Lallai ne talauci ya fi saurin isa ga mai so na (don jarabawa), fiye da ambaliyar ruwa daga saman dutse zuwa ƙasa." (Silsilatus Sahiha: 2828)
    Hadisi
    Manzon Allah (SAW) ya ce: "Lallai ne bala'o'i sun fi saurin isa ga mai so na (don jarabawa) fiye da isar ambaliyar ruwa zuwa ga ƙarshensa." (Silsilatus Sahiha: 1586)
    Hadisi
    Manzon Allah (SAW) ya ce: "Lallai ne na gani ana yi muku jarabawa a cikin ƙaburbura. Tsananinta yana kama da na fitinar Ad-Dajjal." (Muslim: 903; Nasa'i: 1475)
    Hadisi
    Barka da Juma'a 🕌💐

    Manzon Allah (SAW) ya ce: "An yi min wahayin cewa za a muku jarabawa a ƙaburbura. Tsananinta yana kusa da na fitinar Ad-Dajjal!" (Al-Bukhari: 7287; Muslim: 903)
    Hadisi
    Barka da Juma'a 💐

    Jabir Ibn Abdullahi ya ce: "Manzon Allah ya hana a yi fenti a ƙaburbura, ya hana yin gini a kansu, kuma ya hana wani ya zauna a kansu." (Sahihun Nasa'i: 2027)
    Hadisi
    Juma@t Mubarak 💐🕌

    Manzon Allah (SAW) ya ce: "Mutanen da idan mutumin ƙwarai ya rasu suke gina masallaci a kan ƙabarinsa, su ne mafi sharrin halittu ga Allah a ƙiyama." (Al-Bukhari: 427)

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.