Addu'ar Samun Kariyar Allah Daga Dukkan Chututtukan Zuciya (Hassada Hiqdu Munafunci Da Sauran Su)

    TAMBAYA

    Assalamualaikum malam Dan Allah addu'ar mutum ya dinga jin alamun Yana wa wani hassada

    AMSA

    ALHAMDULILLAH

    TUNATARWA GA MASU YIN HASSADA

    Hassada babban ciwone da ya ke chutar da mai yinsa sama da Wanda akeyiwa hassadar, domin hassadar mai hassada bata hana faruwar abin da Allah ya tsara zai faru da bawan sa, don haka wajibi ne a gare mu, mu zama masu farin ciki akan dukkan abun da Allah ya bawa yan'uwan mu, kuma muma mu naimi rabanmu daga wajan Allah sai Allah ya rufamana asirin mu ya kuma fuwace mana ya wadata mu, kuma hakan shine abun da zai sa mu sami kwanciyar hankali a rayuwar mu.

    YA kai mai hassada ka sani kamar kana tuhumar Allah ne akan mai ya sa yabawa wani kaza kai bai baka ba, alhalin Allah shine mai rabawa kowa abin da ya dace da shi, kuma ba mai sa shi ya chanza abin da ya tsara sai dai in shi ya so ya chanza, to don haka kai mai hassada kasani  babu abin da zai chanza sai abin da Allah ya so ya chanza, in ka ci gaba da hassadar kai ne zaka cigaba da zalunta da chutar da kaka.

    WADANNAN ADDU'O'IN SUNA DA TASIRI SOSAI WAJAN ALLAH YA MAGANCEWA MAI YINSU DUKKAN WASU CHUTUTTUKAN DA KE ZUCIYAR SA IN SHA ALLAH, MU KARANTA SU DA YAQININ ALLAH ZAI YAYE MANA MATSALAR DA TAKE CIKIN ZOCIYAR DUKKAN WANDA YA LAZIMCI YINSU SOSAI

    اللَّهُمَ طَهِّرْ قَلْبِي مِن كُلِّ سُوءٍ، اللَّهُمَ طهر قَلْبِي مِن كُلّ مَا يَغْضَبُكَ اللَّهُمَ طَهِّر قَلْبِي مِنْ كُلِّ غِلِّ وَحِقْدٍّ وَحَسَدٍ وكِبَرٍ وَ نَحو ذَلِكَ،

    YA ALLAH KA TSARKAKE MIN ZUCIYATA DAGA DUKKAN ABU MUMMUNA, YA ALLAH KA TSARKAKE MIN ZUCIYA TA DAGA DUKKAN WANI ABUN DA ZAI SANYAKA MUFUSHI, YA ALLAH KA TSARKAKE MIN ZUCIYA TA DA GA DUKKAN QETA DA HIQDU DA HASADA DA GIRMAN KAI  DA MAKAMANTAN SU.

    اللَهُمَّ يَا مُقَلِّبُ القُلُوبَ ثَبِّتْ قَلْبِي عَلىٓ دِينِكَ، وَيَا مُصَرِّفُ القُلُوبَ صَرِّفْ قَلْبِي عَلَى طَاعَتِكَ.

    YA ALLAH MAI JUJJUYAR DA ZUKATA KA TABBATAR DA ZUCIYA TA AKAN ADDININ KA,  YA MAI SARRAFA ZUKATA KA SARRAFA ZUCIYATA AKAN BIYAYYAR KA.

    اللَهُمَّ أَصْلِحْ قَلْبِي  وَعَمَلِي

    YA ALLAH KA GYARAMIN ZUCIYA TA DA KUMA AIYUKANA

    WALLAHU A'ALAM

    AMSAWA {ABU ABDULLAH}

    DAGA ZAUREN FIQHU 07064213990

     ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
    https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

     https://t.me/TambayaDaAnsa

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.