Wacce Irin Tahiyya Kake A Sallar Ka

    TAMBAYA (160)

    Pls tahiya: attahiyyatulillah wassalawatu waddaiyyibah assalamu alayka.....

    Da kuma Attahiyyatulillah azzakiyatulillah  assalamu alayka ayyhannabiyyu......

    Pls wanne ne daidai

    AMSA

    Tashahhud kala 6 ne kamar yanda ya tabbata daga Sunnah. Tahiyyah irinta

    1️) Nana Aisha

    2️) Abdullahi Ibn Abbas

    3️) Abdullahi Ibn Umar

    4️) Abdullahi Ibn Mas'ud

    5️) Abu Musa al-Ash'ariy

    6️) Umar Ibn al-Khattab

    Wadda ka turo itace irin Tahiyyar Abdullahi Ibn Mas'ud da Abdullahi Ibn Umar da mahaifinsa da Kuma Abu Musa al-Ash'ari

    Ta biyun Kuma mai lafazin "Azzakiyatulillah..." itace Tahiyyah irin wadda Annabin Rahama Sallallahu alaihi wasallam ya koyawa Uwar Muminai Sayyada Aisha

    Allaah ya qara musu yarda baki dayansu

    Muhallish shahid dai shine: Dukkansu sun tabbata daga Ma'aiki Sallallahu alaihi wasallam Kuma an so ka dinga kowacce cikin 6 din domin koyi da Sunnonin gaba daya

    Duba: littafin Ibn Abi Shaybah (1/293), al-Saraj, al-Mukhillas, da Kuma Bayhaqi (2/144)

    Tahiyyar da na fi yi, itace

    اَلتَّحِيَّاتُ ِللهِ وَالصَّلَوَاتُ والطَّيِّبَاتُ، اَلسَّلاَمُ عَلَيْكَ  أَيُّهَا النَّبِيُّ  وَرَحْمَةُ اللهِ وَبَرَكَاتُهُ، اَلسَّلاَمُ عَلَيْنَا وَعَلَى عِبَادِكَ الصَّالِحِينَ. أَشْهَدُ أَنْ لاَ إِلَهَ إِلاَّ اللهُ، وَأَشْهَدُ أَنَّ مُحَمَّداً عَبْدُهُ وَرَسُولُه .

    "Attahiyyatu lillahi wassalawatu wattayyibat, assalamu alayka ayyuhan-nabiyyu warahmatul-lahi wabarakatuh, assalamu 'alayna wa'ala ibadil-lahis-saliheen. Ash-hadu an la ilaha illal-lah, wa-ashhadu anna Muhammadan 'abduhu warasooluh."

    Ma'ana

    Dukkan nau'in ban girma ya tabbata ga Allah, da kuma salloli da kyawawan kalmomi. Aminci ya tabbata gare ka ya Annabi, da rahamar Allah da albarkatunsa. Aminci ya tabbata gare mu, da kuma ga bayin Allah salihai ina shaidawa cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah. Kuma ina shaidawa cewa Muhammad bawansa ne kuma Manzonsa ne.

    Karin bayani Kuma zai zo filla filla a cikin karatun da muka Fara last week na littafin GYARAN SALLAH da sauransu

    Mai buqatar shiga USMANNOOR ONLINE ACADEMY, sai yayi magana ta private don kada karatun da muka fara yayi maka nisa

    Wallahu taala a'alam

    Subhanakallahumma wabi hamdika ash-hadu anla'ilaha illa anta astaghfiruka wa'atubi ilayk

    Amsawa

    ✍️ADMIN: ZAUREN TAMBAYA DA AMSA

    Usman Danliti Mato (Usmannoor_Assalafy)

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
    https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

     https://t.me/TambayaDaAnsa

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.