Zan Iya Kitso A Wajen Mace Christian

    TAMBAYA (161)

    Assalamualaikum. Malam Barka da yini Mlm Inada Tambaya Malam yahalata Inje wajen Wadda Ba musulmaba Wanki Kai saboda Anan Bida Bamusulmai masuyi. Ngd

    AMSA

    Waalaikumus Salam Warahmatullahi Wabarakatuhu

    *_Akwai kyakkyawar alaqar kasuwanci tsakanin Kafiran Medina da Musulmai a zamanin Ma'aiki Sallallahu alaihi wasallam

    An haramta kashe Kafirin Amana wanda ya biya Jizya

    Yin kitso a wajen Wanda ba musulmi ba ko wani abu makamancin hakan ba laifi bane ba indai har akwai kyakkyawar alaqa tsakaninki dasu

    Kuma Albishinki - Da nice ke to da Da'awah zanyi Mata !

    Zaki iya amfani da wannan damar wajen kwadaitar da ita ladubban addininki na musulunci

    Misali: Idan zata fara yi Miki kitson sai ke kiyi Bismillah (taji Bismillar) sannan kice Mata ta fara ta bangaren dama domin koyi da Sunnar Ma'aiki Sallallahu alaihi wasallam ta damaitawa

    Idan farce ne Kuma sai ki furta (Bismillahi ala sunnati Rasulullah) ki fada yanda zata ji daganan sai a fara yanke manuniya (yatsa) sai a damaita, bazaa yanke babban dan yatsa na dama ba tukunna don gudun kada a dawo hagu, sai a dauko yatsun hagu a damaita su a qare da babban yatsan Daman. Kinga kinyi koyi da Matan Ma'aiki Sallallahu alaihi wasallam da Kuma Matan sahabbansa (Radiyallahu anhuma)

    Idan Kuma Lalle/Kunshi ne ko Subqa zatayi Miki sai shima kiyi Bismillar sai ta fara miki da kafar dama a kammala da ta hagu

    Zaki Sha tambaya a wajenta kam. Sai ka bata amsa da ai wannan shine Sunnar Dan uwan Annabi Isah (Alaihis Salam) da aka turawa Nasara yan kauyen Nazreth dake kasar Palestine shekaru sama da 2,000 da suka shude

    Daganan sai hira ta barke !

    Ki rufe ta da hujjoji !

    La'alla ta musulunta a hannunki tunda suna yunwar neman hujjar da zata sadasu zuwa ga Gaskiya sabanin Yahudawan da sun san gaskiyar musulunci amman suka take silar hakan suka bata. Nasara suna cuna cikin duhun jahilci shiyasa suka zamo batattu su Kuma Yahudu Kuma son zuciya da take qarya shiyasa Allaah Azzawajallah yayi fushi dasu. Kuma shiyasa a kullum a kalla muke maimaita ayar dake cikin Suratul Fatiha su 17 (Farillai):

    ( اهْدِنَا الصِّرَاطَ الْمُسْتَقِيمَ )

    الفاتحة (6) Al-Faatiha

    Ka shiryar da mu ga hanya madaidaiciya.

    ( صِرَاطَ الَّذِينَ أَنْعَمْتَ عَلَيْهِمْ غَيْرِ الْمَغْضُوبِ عَلَيْهِمْ وَلَا الضَّالِّينَ )

    الفاتحة (7) Al-Faatiha

    Hanyar waɗanda Ka yi wa ni'ima, ba waɗanda aka yi wa fushi ba, kuma ba ɓatattu ba.

    Bawai dole bane ki fada Mata hakan Amman koyi da Sunnah ne domin kuwa Babu dole a addini kamar yanda Allaah Azzawajallah ya fada

    ( لَا إِكْرَاهَ فِي الدِّينِ ۖ قَد تَّبَيَّنَ الرُّشْدُ مِنَ الْغَيِّ ۚ فَمَن يَكْفُرْ بِالطَّاغُوتِ وَيُؤْمِن بِاللَّهِ فَقَدِ اسْتَمْسَكَ بِالْعُرْوَةِ الْوُثْقَىٰ لَا انفِصَامَ لَهَا ۗ وَاللَّهُ سَمِيعٌ عَلِيمٌ )

    البقرة (256) Al-Baqara

    Bãbu tĩlastãwa a cikin addini, haƙĩƙa shiriya tã bayyana daga ɓata; Sabõda haka wanda ya kãfirta da dãgũta kuma ya yi ĩmãni da Allah, to, haƙĩƙa, yã yi riƙo ga igiya amintacciya, bãbu yankwa agare ta. Kuma Allah Mai ji ne, Masani.

    Karin bayani Kuma zai zo filla filla a cikin karatun da muka Fara last week na littafin SUNNONI 1,000+ da sauransu

    Mai buqatar shiga USMANNOOR ONLINE ACADEMY, sai yayi magana ta private don kada karatun da muka fara yayi maka nisa

    Wallahu taala a'alam

    Subhanakallahumma wabi hamdika ash-hadu anla'ilaha illa anta astaghfiruka wa'atubi ilayk

    Amsawa:

    ✍️ADMIN: ZAUREN TAMBAYA DA AMSA:

    Usman Danliti Mato (Usmannoor_Assalafy)

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
    https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

     https://t.me/TambayaDaAnsa

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.