Manzanni Ashirin Da Biyar

    MANZANNI 25

    Farko da sunan Allah
    Hakimu Jalla Jalalah
    Shakur abin madallah
    Kyautarshi dalla-dallah
    Shine Wahabu Sarki Allah.

    Ni Madaki sarauta
    Nayi nufin na rubuta
    Batu akan Magabata
    Manzanni ‘yan gata
    Kaji masoyan Sarki Allah.

    Ya jama’a fa ku ganni
    Kira nake fa kuji ni
    Ko a cikin Kur’ani
    Akwaishi fanni-fanni
    Batu akan Manzannin Allah.

    Adamu Baba Ubana
    Batunka yau zan zana
    Uba na kakannina
    Uwa -Uban dangina,
    Adamu kakan Manzon Allah.

    Da na duba da na hanga
    Da na juya da na waiga
    A duniyarnan wagga
    Babu uba ko Oga
    Wajenka Adamu Manzon Allah.

    Allah Shi Ya yiyo ka
    Mala'iku a gareke
    Sujud sukai wa kamarka
    Aljanna kai da gwanarka
    Tazam masaukin Manzon Allah.

    Sai Idirisu fa nawa
    Gareshi zan juyawa
    Idi mutum dan mowa
    Shi aka yo wa dagawa
    Zuwaga Sarki Maliku Allah.

    Alkaluma ya feke
    ittatafa ya mike
    Anan ya samo like
    Idi, uba gun Zulke
    Madaukaki kuma bawan Allah.

    Taurarin da ka hanga
    Iliminsu shi ya kaga
    Lissafi yaka kirga
    Harda fa dinkin riga
    Duk da nufin Mahalicci Allah.

    Saifa Nabiyyin Allah
    Mai wa’azi abi Allah
    Yay hakuri dan Allah
    Nuhu abin madallah
    Akan kira gun Sarki Allah.

    Nayi nufin jan carbi
    Akan uban duk arabi
    Mai zuri’a daga Rabbi
    Hamu da Yafizu dubi
    ‘Yayane gun Manzon Allah.

    Zan daga sauti nawa
    Na addu’a gun bawa
    Ni bani son mantawa
    Da Nuhu mai juyawa
    Akan ruwan Dufanar Allah.

    Hudu da Salihu nawa
    Suma sunci yabawa
    Manzannin Adawa
    Samuda masu adawa
    Kan addinin bautar Allah.

    Mu dai munyi maraba
    Da zuwan Hudu da Baba
    Salihu mai son Rabba
    Madaki mai abarba
    Dauki shirin bin bayin Allah.

    Na daga hannu Allah
    Ka kara tsira Jallah
    Akanshi Hudu Nasallah
    Annabi Salihu jimlah
    Madaukaka gun Sarki Allah.
     
    Zanyi rubutun alli
    Yabo ko dadai hali
    Akan mutum mai kwalli
    Ibrahimu Kalili
    A wajen mai yin mulki Allah.

    Ya bi umarnin Sarki
    Maliku mai yin mulki
    Anan ya samu mataki
    Ibrahimu na kirki
    Imamu gun duk bayin Allah.

    Bani da ikon karta
    Batun uban magabata
    Dan kuwa yayi nagarta
    Ka’aba shi ya ginata
    Gami da layyar idin Allah.

    Annabi Ludu alaika
    Rahamar Allah kanka
    Manzanci a hanunka
    Ka fi uba sai kaka
    Kokuma kakan Manzon Allah.

    Matarshi ta ki yarda
    Da abinda shi ya yarda
    Sai Allah ko ya yarda
    Da shi cikakken yarda
    Ya bashi sakon tsoron Allah.

    Mala’iku suka zo su
    Wajenshi Ludu da kansu
    Mabarnata ko dukansu
    Nufinsu tozarta su
    Sai aka kona kazamai, Allah!

    Isma’ilu alaika
    Sallallahu wa Baraka
    Ruwanka babu da jaka
    Ko mara niyyar Zakka
    Kai kayi salla domin Allah. 

    Allah yai maka gata
    Ka’aba dakai gininta
    Zamzam ma tushenta
    Isma’ilu na Mutta
    Sannan Da gun Manzon Allah.

    Allahu ya yabaka
    Hakuri babu kamarka
    Safa da Marwa a kanka
    Farauta tun daga kanka
    Tazam sana’ar bayin Allah.

    Alhaji dauki shirinka
    Akan yabon Manzonka
    Koko kace mar Kaka
    Ishaku kam son barka
    Mai ilimi gun bayin Allah.

    Mala’ika Jibirilu
    Dashi da Mika’ilu
    Suka je gunshi Kalilu
    Ibrahimu Rasulu
    Akan busharar Manzon Allah.

    Ishiyaku 'Da Alimu
    Allah ma fa karimu
    Yayi kiransa Alimu
    Dan ya zo shi da ilmu
    Akan umarnin Sarki Allah.

    Zuwa ga danka Ubana
    Madaki dan gurfana
    Amma cikin lumana
    Dan baya son barna
    Yakubu Baban Manzon Allah.

    Yayi nasiha babba
    Tun daga Da har Baba
    Da dukka mai yin gaba
    Da Danshi Manzon Rabba
    Yakubu tsoho mai son Allah.

    Yayi Makantar kunci
    Kuka ko harda na zuci
    Domin yanada takaici
    Batan diyanshi maceci
    Yusufu Dan Manzannin Allah.

    Yau ‘yan amshi gani
    Da ni da Zulhusunaini
    Yusufu mai kyan badani
    Na Rabbi 'Dan Manzanni
    Yusufu 'Da mai tsoron Allah.

    Yusufu 'Dan Ya’akuba
    Nayi maraba da tarba
    Dan nayi murnar tsaraba
    Ba kwai ba koko abarba
    Sai dai tsoron Sarki Allah.

    Ru’uya yai ta’awili
    Awu ko yai ta da kaili
    Mulkinshi babu falli
    Sannan shifa Kalil
    Yaki jinin mai sabon Allah.

    Allah ka bani dama
    In yabi Manzon fama
    Manzo ne mara rama
    Shu’aibu mai yin hikima
    Wujen isar da wasikar Allah.

    Yayi bayani sosai
    Akan awun cin kosai
    Mudun ma na gilasai
    Dadin zance kuma sai
    Shuaibu bawan sarki Allah.

    Allah na roke ka
    Da dukkanin sunanka
    Ka kara tsirar gunka 
    Kan Manzon da ka aika
    Madyana birnin sabon Allah.

    Adole yau zan zauna
    In yabi Manzon guna
    Kallamu Musa ubana
    Haruna ko kakana
    Kaji mazajen Sarki Allah.

    Haaruna kai da Musa
    Kunyi jihadin fansa
    Allah yayi nufinsa 
    Ayoyi tara an sa
    Akansu arnan bautar Allah.

    Fir’auna kayi dagawa
    Hamana kayi adawa
    Akanshi Musa nawa
    Karuna kaiko wawa
    Kaki ciyarwa domin Allah.

    Allah ya daukaka ku
    Aljannarsa ya baku
    Haruna ne babbanku
    A haife banda zuwanku
    Isarda sakon Sarki Allah.

    Tun banji kasala ba
    Ya dace nayi duba
    Ga makerina babba
    Dawud nayi maraba
    Sannu da himma Manzon  Allah.

    Yayi umarnin sallah
    Yay shari’a dan Allah
    Alkali mai kamalah
    Dawud mai yin sallah
    Tsakan dare dan Sarki Allah.

    Ai huduba a wajenshi
    Aka samo ta zuwanshi
    Zabbura a hanunshi
    Azumi ko tun a kanshi
    Tai falala inji Manzon Allah.

    Santsi ya debeni
    Na fadi gun mai bani
    Shine dan husunaini
    Mulkinshi babu raini
    Sannu Sulaiman Manzon Allah.

    Baiwarsace ta sani
    Nayo rubutun karni
    Yay mulkin shaidani
    Mutum da tsuntsun tsauni
    Da daukakar Mabuwayi Allah.

    Iska ce motarshi
    Aljan ko bawanshi
    Sarauniya matarshi
    Duk kwari sun sanshi
    Kaji Sulaiman bawan Allah.

    Allah bani basira
    In yabi Manzon tsira
    Ayuba mai kyan sura
    Bai da nufin almara
    Wajen biyayyar Sarki Allah.

    Jarabawa daga Jalla
    Ta riski bawan Alla
    Shaidan ne mara salla
    Ya shafi Manzon Allah
    Ayuba dattijo gun Allah.

    Allah yayi kiransa 
    Sabiru koko da Hausa
    Mahakurci wan kasa
    Domin ya dau fansa
    Rashin gazawa domin Allah.

    Zilkiflu mai sona
    Yabonka yau zan nuna
    Halinka zan tattauna
    Manzon Ubangijina
    Maliku Sarkin bayin Allah.

    Duk wani bawan Allah
    A zamaninka na sallah
    Sun buya dan mara sallah
    Ta nan ka samu kamalah
    Zilkiflu mai kaunar Allah.

    "Zil" ma’aboci kenan
    "Kiflu" ko reno kenan
    Zuwa ga hausa fa kenan
    Dan haka shine wannan
    Mai renon Manzannin Allah.

    Yunusa Manzon tsira
    Ya zama dole na tsara
    Yabon dab a almara
    Domin ka sha madara
    A rakumar gun tekun Allah.

    Kayi fishi dan Allah
    Kan jirgi kayi sallah
    Kuri’a da nufin Allah
    Ta nuna Manzon Allah
    A cikin dubban bayin Allah.

    Ni Madaki muhti
    Zan yabi bakon huti
    Tasbihinsa da kati
    Anan ya samu mataki
    Cikin gidan aljannar Allah.

    Sai wa na Iliyasu
    Mai wa’azi ga dukansu
    Arna masu yawansu
    Koko nace maka masu
    Bautan gunki wai shi Allah.

    A Ba’alabak suka zauna
    Da shi da dangin bauna
    Ba’a'ala mai kan waina
    Dan sun rikeshi da kauna
    A maimakon Mahalicci Allah.

    Ni’imar Allah kanka
    Shi ya kira sunanka
    Ilyasu kakan kaka
    Mudi zashi wajenka
    Ka tsakura mai tsoron Allah.

    Cikin dabara zan je
    Na gaida mai kyan saje
    Yasa’u ka fi mazaje
    Kaifinka ya fi na lauje
    Wajen isar da wasikar Allah.

    Alyasa’u Manzo ne
    Cikin dubu kwara ne
    Cikar sani wahayi ne
    Dan haka mai ilimi ne
    Annabi ne gun Sarki Allah.

    Tahiyyati hannunka
    Kasidati dominka
    Muhibbati kallonka
    Yasa’u komai naka
    Sannu Nabiyyul Lahi na Allah.

    Zani kiran Zakariyya 
    Annabi ne mara karya
    Danginshi babu karya
    Shi ne baban Yahaya
    Sannan dattijo gun Allah.

    Bautarshi babu wasa
    Yarenshi sak da Hausa
    Kuri’arshi yaci gasa
    Maryam innar Isa
    Duk a hanun Zakariyan Allah.

    Allah yayi kiranshi
    Da shi da duk zuri’arshi
    Zakariyya da diyanshi
    Tare da ma matarshi
    Wajen ibadar Sarki Allah.

    Yahaya ja ni wajenka
    Na shafi dan girmarka
    Annabci a hanunka
    Tun a gadon innarka
    Kaji masoyin Sarki Allah.

    Sallal Lahu alaika
    Da kai da ma babanka
    Nifa ina kaunarka
    Ka bani dammar binka
    Cikin gidan aljannar Allah.

    Isa mai Linjila
    Kaunarka ce yau zalla
    Tasa nayo ma kwalla
    Begenka na malala
    Kan Mahamud mai tsoron Allah.

    Ya warkas da makafi
    Kuturu har mara tafi
    Kurma Da da mahaifi
    Har gawa mara karfi
    Tay magana da Ma’aikin Allah.

    Dan Maryam Manzo ne
    Wajen Nasara Amir ne
    Gun Allah bawa ne
    Isa marar baba ne
    Tamkar Adamu Manzon Allah.

    Bani tunanin gunka
    Da dukkanin natsuwarka
    Zan yabi Manzon Makka
    Muhammadun na so ka
    Sannu fiyayyen bayin Allah.

    Duk acikin Manzanni
    Kai ka zamo murjani
    Kai aka ba Kur’ani
    Sarkin Hurul aini
    Muhammadun mai tsoron Allah.

    Yay hijira da Sahabbai
    Jikinsu babu takubbai
    Sunje basu da kwabbai
    In karya ne tambai
    Masu nasiha domin Allah.

    Ya ma’abocin sallah 
    Bashiru bawan Allah
    Ka ceci bayin Allah
    A randa ba wani haulah
    Sai a wajen Mahalicci Allah.

    Sannu madubi babba
    Ga dukka Da har baba
    Wanda yace ba kai ba
    Aradu ba tababa
    Zai ga azabar Sarki Allah.

    Ni na kara salati
    Wajenka mai kyan zati
    Kafin inyi wafati
    Ni Madakin baiti
    Na gode maka Sarki Allah.

    Na yabi duk manzanni
    Su suka zo Kur’ani
    Sai ku rikesu ku barni
    Ni a Misau aka yo ni
    Birnin bautar Sarki Allah.

    Wallahul Musta'an!!!
    Mal. Mahmudul Kalaam

    Mal. Mahmudul Kalaam 
    17 October, 2014

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.