Ticker

    Loading......

Marigayi Alhaji Umar Adamu (ALhaji Sanda Adamu Tsafe)

Marigayi Alhaji Umar Adamu (ALhaji Sanda Adamu Tsafe)
An haifi Alhaji Umar Adamu da aka fi sani da Alhaji Sanda Adamu Tsafe a garin Tsafe, Jihar Zamfara a shekarar 1948. Ya yi karatun addinin Musulunci da na zamani a garin Tsafe. Ya halarci  LEA Primary School, Tsafe da Senior Primary School, Kwatarkwashi da Makarantar Lardi ta Sakkwato (Nagarta College) da SBS /Ahmadu Bello University, Zaria da School of Journalism ta London inda ya koyi aikin Jarida.
Ya yi aikin Jarida a Gidan Rediyon BBC London da Radio Nigeria Kaduna har ma ya riƙe muƙamin Babban Manajan Gidan Rediyon Rima na Gwamnatin Jihar Sakkwato. Ya kuma riƙe  muƙamin Kwamishinan Zaɓe  mai kula da Birnin Tarayya, Abuja a Hukumar Zaɓe ta Ƙasa. 
Masarautar Tsafe a lokacin mulkin Marigayi Mai martaba Yandoton Tsafe, Alh. Habibu Aliyu ta karrama shi da Sarautar "Sarkin Yaƙin Tsafe". Mutum ne mai himma da  hazaƙa  da basira da ya bayar da gudunmuwa wajen ci gaban addinin Musulunci da aikin jarida da kuma al'ummarsa.
Ya rasu a ranar Asabar, 8/2/25 yana da shekaru 77 a duniya, a Asibitin Koyarwa ta Jami'ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sokoto sanadiyar rashin lafiya. Ya bar matan aure 2 da ya'ya /ɗiya 29 da jikoki 36. Allah ya jiƙan sa da rahama, amin.

Ibrahim Muhammad Ɗanmadamin Birnin Magaji, Jihar Zamfara.
08149388452, 08027484815
birninbagaji4040@gmail.com
Lahadi, 09/02/2025.

Post a Comment

0 Comments