DA MUNGUWAR RAWA GARA ƘIN TASHI… (7)
KARIN DALILAI DA SUKE TABBATAR DA CEWA: AQIDAR
SAYYID QUTUB TA KHAWARIJAWA CE
Idan ba a manta ba, tun bayan lokacin da masu kare barnar Sayyid Qutub suka fara tuhumar Manyan Malaman Sunna da Akidar Sayyid Qutub ta "Hakimiyya" muka yi kokarin banbance tsakanin tafarkin Sayyid Qutub daga tafarkin wadancan Malamai ta hanyar bayyana Akidarsu ta Sunna, shi kuma muka tabbatar da cewa Akidarsa ta Khawarijawa ce, saboda dalilai kamar haka
1- Kasancewar ya tabbatar da Akidar Khawarijawa a
"Hakikanin Imani", wato ya ce: Imani abu ne guda daya dunkulalle, ba
ya rarrabuwa, idan mutum ya bar wani yanki nasa to ya fita daga Muslunci.
2- Kasancewar ya kafirta dukkan al'ummar Musulmi,
don cewa ya yi: dukkan Mutanen Duniya (البشرية) gaba
daya sun koma Jahiliyya sun yi ridda daga Addinin Muslunci.
To a yau kuma da iznin Allah za mu kara kawo wasu
dalilan ne da suke kara tabbatar da Akidar tasa ta Khawarijawa ce. Ga su kamar
haka
1) Sukarsa ga mas'alar karuwar Imani da raguwarsa.
2) Kore samuwar Mumini mai raunin Imani.
3) Ba ya ganin halascin Sallar Juma'a.
4) Yankan Musulmai kamar yankan Ahlul Kitabi ne,
saboda ba musulmai ba ne.
Kowane daya daga cikin wadannan yana daga cikin
Akidun Khawarijawa, wadanda rassa ne na abubuwa guda biyu da muka ambata a baya
na tushen Khawarijanci.
Za mu dauki wadannan daya bayan daya mu tabbatar
da su da iznin Allah.
(1) SUKAR AKIDAR KARUWAR IMANI DA RAGUWARSA
Abu ne sananne a Akidar Ahlus Sunna cewa Imani
yana karuwa kuma yana raguwa, saboda dalilai masu yawa na Shari'a. Saboda su
Ahlus Sunna a wajensu Imanin rassa ne, yana rarrabuwa. Kamar yadda Annabi (saw)
ya ce
«الإيمان بضع وستون شعبة، والحياء شعبة من الإيمان» وفي
رواية: «بضع وسبعون شعبة».
صحيح البخاري (1/ 11) صحيح مسلم (1/ 63)
((Imani rassa sittin da wani abu ne, - ko saba'in
da wani abu - kunya reshe ne na Imani)).
Shaikhul Islami yana bayanin tushen da a kansa
Ahlus Sunna suka gina Akidarsu a Hakikanin Imani sai ya ce
((وأصلهم أن الإيمان يتبعض فيذهب بعضه ويبقى بعضه كما في قوله
عليه الصلاة والسلام {يخرج من النار من كان في قلبه مثقال ذرة من إيمان}، ولهذا
مذهبهم أن الإيمان يتفاضل ويتبعض، هذا مذهب مالك والشافعي وأحمد وغيرهم)).
مجموع الفتاوى (18/ 270)
((Tushen Akidar Ahlus Sunna; Imani yana rarrabuwa,
sashensa yana tafiya, sashe ya saura, kamar yadda Annabi (saw) ya ce: {Wanda
akwai kwatankwacin kwayar zarra na imani a zuciyarsa zai fita daga wuta (ba zai
dawwama a cikinta ba, saboda shi ba kafiri ba ne)}. Wannan ya sa Mazhabar Ahlus
Sunna ita ce: Imani yana fifiko, kuma yana rarrabuwa, wannan shi ne Mazhabar
Malik, Shafi'iy da Ahmad da wasunsu)).
A dalilin Imani yana rarrabuwa rassa – rassa shi
ya sa ya zama za a iya rasa reshi na imanin, sai imanin ya ragu, idan kuma
wannan reshen da aka rasa ya dawo sai imanin ya karu. Maganganun jagororin
Sunna a kan haka suna da yawa, inda suka ce: «الإيمان قول وعمل،
يزيد وينقص، حتى لا يبقى منه شيء»
Saboda Nassoshi masu yawa da suka zo suka tabbatar
da haka.
Amma kasancewar Murji'a da Khawarijawa da
Mu'utazila sun gina Akidarsu game da Hakikanin Imani a kan cewa; Imani abu ne
guda daya a dunkule, ba ya rarrabuwa, shi ya sa suka ce: Imanin ba ya karuwa,
kuma ba ya raguwa. Sai Murji'a suka ce: Idan bangare na Imanin ya tabbata ga
mutum to cikakken Imanin ya tabbata. Su kuma Khawarijawa da Mu'utazila suka ce:
Idan bangare na Imani ya tafi, aka rasa shi to an rasa Imanin gaba daya, mutum
ya zama kafiri. Shi ya sa suke kafirta duk wanda ya aikata sabo. Khawarijawan zamani
kuma, wadanda suka tasirantu da Fikrorin Sayyid Qutub suke kafirta Musulmai da
abin da bai kai kafirci ba, karkashin Mafhumin "Hakimiyya" a wajensu.
Wannan ya sa a wajen Murji'a da Khawarijawa Imani
ba ya raguwa kuma ba ya karuwa, sai suka saba ma Alkur'ani da Sunna da Ijma'in
Salaf Ahlus Sunna a kan haka.
To idan mun duba mas'alar a wajen Sayyid Qutub
kuma za mu ga shi kuma bai ba wa mas'alar muhimmanci ba, sai ya nuna cewa;
kawai wata kadhiyya ce ta Ilmul Kalam, aka tattauna ta lokacin walwalar hankali
da kuma rashin bai wa aiki muhimmanci. Ya fadi haka ne a "hashiya" a
cikin littafinsa, inda ya ce
((هنا تعرض قضية: «الإيمان يزيد وينقص» وهي قضية من قضايا
الفرق وقضايا علم الكلام في فترة الترف العقلي والفراغ من الاهتمامات العملية
الجادة.. فلا ندخل نحن الآن فيها!!!))
في ظلال القرآن (3/ 1475)
Lallai wannar magana ba dadai ba ce, mas'alar
karuwan Imani da raguwarsa Alkur'ani da Sunna ne suka zo da ita, Salaf suka yi
Ijma'i a kanta. Babu masu inkarinta ko sukarta sai 'Yan Bidi'a.
(2) KORE SAMUWAR MUMINI MAI RAUNIN IMANI
Mas'alar farko da aka fara sabani a kanta a cikin
al'umma ita ce mas'alar "Mumini mai sabo", inda al'umma ta kasu kashi
uku
a) Khawarijawa suka ce: Mutane biyu ake da su,
Imma Mumini ko Kafiri.
b) Mu'utazilawa su ma suka ce: Mutane biyu ake da
su, Imma Mumini ko kuma wanda yake "Manzila baina Manzilataini",
wato; wanda ya fita daga Imani amma bai shiga kafirci ba. Ma'ana; yana tsakanin
Imani da kafirci.
c) Su kuma Ahlus Sunna suka ce: Mai sabo Mumini ne
amma mai tauyayyen Imani.
Ibnu Taimiyya yana bayanin Akidar Ahlus Sunna a
cikin "Wasidiyya" sai ya ce
((ولا يسلبون الفاسق الملي اسم الإيمان بالكلية ولا يخلدونه
في النار كما تقوله المعتزلة، بل الفاسق يدخل في اسم الإيمان في مثل قوله تعالى:
{فتحرير رقبة مؤمنة}، وقد لا يدخل في اسم الإيمان المطلق كما في قوله تعالى: {إنما
المؤمنون الذين إذا ذكر الله وجلت قلوبهم وإذا تليت عليهم آياته زادتهم إيمانا}،
وقوله صلى الله عليه وسلم: {لا يزني الزاني حين يزني وهو مؤمن ولا يسرق السارق حين
يسرق وهو مؤمن ولا يشرب الخمر حين يشربها وهو مؤمن ولا ينتهب نهبة ذات شرف يرفع
الناس إليه فيها أبصارهم حين ينتهبها وهو مؤمن}. ويقولون: هو مؤمن ناقص الإيمان،
أو مؤمن بإيمانه فاسق بكبيرته؛ فلا يعطى الاسم المطلق، ولا يسلب مطلق الاسم)).
مجموع الفتاوى (3/ 151 - 152)
A wani wajen kuma ya ce
((قوله صلى الله عليه وسلم: {لا يدخل الجنة إلا نفس مؤمنة}
حق، إذا أريد به الدخول المطلق الكامل أريد بالمومن الكامل المطلق، وإذا أريد
بالدخول مطلق الدخول فقد يتناول الدخول بعد العذاب، فإنه يراد به مطلق المؤمن، حتى
يتناول الفاسق الذي في قلبه مثقال ذرة من إيمان، فإن هذا يدخل في مطلق المومن
كقوله تعالى: {فتحرير رقبة مؤمنة}، ولا يدخل في المؤمن المطلق كقوله تعالى: {إنما
المؤمنون الذين إذا ذكر الله وجلت قلوبهم وإذا تليت عليهم آياته زادتهم إيمانا}
الآية.
ومثل هذا كثير في الكتاب والسنة ينتفى الاسم عن المسمى تارة
لنفي حقيقته وكماله، ويثبت له تارة لوجود أصله وبعضه)).
مختصر الفتاوى المصرية (ص: 206)
A bayanin Ibnu Taimiyya ya bayyana mana cewa;
Muminai nau'i biyu suke
1. Mumini mai cikakken Imani (المؤمن المطلق)
(المؤمن حقا) (المؤمن كامل الإيمان).
2. Mumini mai tauyayyen Imani (مطلق المؤمن) (مؤمن ناقص الإيمان) (مؤمن بإيمانه فاسق بكبيرته).
To amma shi kuma Sayyid Qutub da ya zo yana magana
a kan wannar Ayar
{إِنَّمَا الْمُؤْمِنُونَ الَّذِينَ إِذَا ذُكِرَ اللَّهُ وَجِلَتْ
قُلُوبُهُمْ وَإِذَا تُلِيَتْ عَلَيْهِمْ آيَاتُهُ زَادَتْهُمْ إِيمَانًا وَعَلَى
رَبِّهِمْ يَتَوَكَّلُونَ (2) الَّذِينَ يُقِيمُونَ الصَّلَاةَ وَمِمَّا
رَزَقْنَاهُمْ يُنْفِقُونَ (3) أُولَئِكَ هُمُ الْمُؤْمِنُونَ حَقًّا} [الأنفال: 2
- 4]
Sai ya kore samuwar duk wani Mumini in ba wanda
yake nau'i na farko ba, wato; Mumini mai cikakken Imani. Inda ya ce
((إن التعبير القرآني دقيق في بنائه اللفظي ليدل دلالة دقيقة
على مدلوله المعنوي. وفي العبارة هنا قصر بلفظ
«إنما» . وليس هنالك مبرر لتأويله- وفيه هذا الجزم الدقيق-
ليقال: إن المقصود هو «الإيمان الكامل» ! فلو شاء الله- سبحانه- أن يقول هذا
لقاله. إنما هو تعبير محدد دقيق الدلالة. إن هؤلاء الذين هذه صفاتهم وأعمالهم
ومشاعرهم هم المؤمنون. فغيرهم ممن ليس له هذه الصفات بجملتها ليسوا بالمؤمنين.
والتوكيد في آخر الآيات: «أُولئِكَ هُمُ الْمُؤْمِنُونَ حَقًّا» يقرر هذه الحقيقة.
فغير المؤمنين «حقاً» لا يكونون مؤمنين أصلاً.. والتعبيرات القرآنية يفسر بعضها
بعضاً. والله يقول: «فَماذا بَعْدَ الْحَقِّ إِلَّا الضَّلالُ» فما لم يكن حقاً
فهو الضلال. وليس المقابل لوصف: «المؤمنون حقاً» هو المؤمنون إيماناً غير كامل!
ولا يجوز أن يصبح التعبير القرآني الدقيق عرضة لمثل هذه التأويلات المميعة لكل
تصور ولكل تعبير!)).
في ظلال القرآن (3/ 1474)
Sai Sayyid Qutub ya nuna cewa; Wannar Ayar ba
magana take yi a kan cikakken Imani ba, kawai duk wanda ba shi da wadannan
Siffofi na Muminai da Allah ya ambata a Ayar to kwata – kwata shi ba Mumini ba
ne. Don haka duk wanda bai zamo Mumini "hakkan" ba to kwata – kwata
shi ba Mumini ba ne. Don haka babu wani abu da yake Imani ba cikakke ba, wanda
yake kishiyar Imani "hakkan".
Ka ga wannan shi yake fassara abin da ya fada
cewa; Imani abu daya ne dunkulalle. Wato shi ne Imanin Muminai
"hakkan". Kuma shi bai ma yarda a kira su da masu cikakken Imani ba,
don shi a wajensa kwata-kwata babu wani Imani wanda ba cikakke ba.
To ka ga maganarsa ta saba Akidar Ahlus Sunna,
tunda ba ta Mu'utazilawa ba ce to ta Khawarijawa ce.
(3) YANKAN MUSULMAI KAMAR YANKAN AHLUL KITABI NE,
SABODA BA MUSULMAI BA NE
Akwai wani mutum mai suna Aliyu Ash'amawiy, wanda
shi ne Kwamandan Rundunar Sirri ta Ikhwan na karshe, wanda ya ba da labarin
irin mummunan tasirin da Fikrorin Sayyid Qutub suka yi wa matasan Ikhwan. A
sakamakon tasirin irin karantarwan da Sayyid Qutub yake yi wa matasan har ya
kai ga suna tunanin zartas da hukunce – hukuncen kafirtawan da yake yi wa
Musulmai, har wata rana wani ya tambayi Aliy Ashmawiy a kan cin yankan wadannan
Musulman, ga abin da ya ce
((جاءنى أحد الإخوان وقال لي: إنه سوف يرفض أكل ذبيحة
المسلمين الموجودين حاليًا، فذهبت إلى الأستاذ سيد قطب وسألته عن ذلك فقال: دعهم
يأكلوها، فليعتبروها ذبيحة "أهل كتاب"، فعلى الأقل المسلمون الآن هم
"أهل كتاب")).
التاريخ السري لجماعة الإخوان المسلمين (ص: 172)
((Daya daga cikin 'yan'uwa ya zo ya ce min: shi
zai bar cin yankan wadannan Musulman da suke nan a yanzu, sai na tafi wajen
Sayyid Qutub na tambaye shi a kan haka sai ya ce: Barsu su ci, su dauki yankan
nasu a matsayin yankan "Ahlul Kitabi", saboda mafi karancin halin
Musulman yanzu su "Ahlul Kitabi" ne)).
To ka ga ya gina rashin cin yankan ne bisa cewa;
su ba Musulmai ba ne.
(4) BA YA GANIN HALASCIN SALLAR JUMA'A
A wata ranar Juma'a Aliy Ashmawiy yana tare da
Sayyid Qutub a gidansa, suna shirin karbo makamai da aka tura musu daga wata
kasa, a wannar ranar ya tabbata masa cewa: Sayyid Qutub ba ya halartan Sallar
Juma'a, saboda yanzu ba lokacinta ba ne, yanzu zamanin Jahiliyya ne, babu
Khalifanci na Muslunci. Ashmawiy ya ce
((وجاء وقت صلاة الجمعة، فقلت له: دعنا نقم ونصلى، وكانت
المفاجأة أن علمت ولأول مرة أنه لا يصلى الجمعة، وقال: إنه يرى فقهياً أن صلاة
الجمعة تسقط إذا سقطت الخلافة، وأنه لا جمعة إلا بخلافة. وكان هذا الرأى غريباً
علي، ولكني قبلته لأنه فيما أحسب أعلم مني)).
التاريخ السري لجماعة الإخوان المسلمين (ص: 209)
((Lokacin Sallar Juma'a ya yi, sai na ce masa:
barmu mu tashi mu je Sallah, abin mamaki da ya faru shi ne a karo na farko
kenan da na san ba ya yin Sallar Juma'a. Sai ya ce: "Shi yana ganin a
Fiqhance, Sallar Juma'a ta fadi idan Khalifanci ya fadi, babu Sallar Juma'a
idan babu Khalifanci".
To wannan ra'ayi ya yi mini banbarakwai, amma sai
na karba a haka, saboda ina ganin ya fi ni ilimi)).
Wannan ya saba ma Akidar Ahlus Sunna.
Imamu Ahmad da Aliyu bnu al-Madiniy suka ce
((وصلاة الجمعة خلفه وخلف من ولى جائزة تامة ركعتين، من
أعادهما فهو مبتدع، تارك للآثار، مخالف للسنة، ليس له من فضل الجمعة شيء إذا لم ير
الصلاة خلف الأئمة من كانوا برهم وفاجرهم)).
شرح أصول اعتقاد أهل السنة والجماعة (1/
181)
((Sallar Juma'a a bayan shugaba - nagari ne ko
fajiri - da bayan Limamin da ya nada ta halasta, cikakkiya ce raka'a biyu. Duk
wanda ya je gida ya sake to Dan Bidi'a ne, ya bar "athaar" ya saba ma
Sunna, kuma ba shi da komai na falalar Juma'ar, matukar ba ya ganin halascin
yin Sallah a bayan shugabanni, nagari suke ko fajirai)).
Ibnu Taimiyya a cikin "Wasidiyya" ya ce
((يأمرون بالمعروف وينهون عن المنكر على ما توجبه الشريعة.
ويرون إقامة الحج والجهاد والجمع والأعياد مع الأمراء أبرارا كانوا أو فجارا)).
مجموع الفتاوى (3/ 158)
((Ahlus Sunna suna umurni da kyakkyawa suna hani a
kan mummuna, bisa ka'idojin Shari'a. Kuma suna da Akidar gabatar da Aikin Hajji
da Jihadi da Sallar Juma'a da Eidi tare da Sarakuna, nagari suke ko fajirai)).
A takaice, da wadannan misalai ya kara tabbata
cewa; Sayyid Qutub Akidunsa na Khawarijawa ne.
✍️ Dr. Aliyu Muh’d Sani (H)
Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.