TAMBAYA (220)❓
Don Allah ina son na san mene ne laifi na don na faɗa wa miji na cewar na bawa kishiyata kwanana la'akari da cewar yau za ta dawo daga wata tafiya da ta yi. Me ya sa ya rufe ni da zagi cewar abin da nake fada wai jahilci ne
AMSA❗
Da farko dai
ina roqon Allaah ya baki ladan wannan manufar taki
Yayinda wasu
suke fada da kishiya wasu kuma suke zuwa wajen boka don a mallake miji a cutar
da kishiya amman ke anan kin duba maslaha ne la'akari da cewar idan kinawa
kishiyar taki kwadayin wannan kwanan ne tunda za ta dawo ne daga tafiyar da
tayi
Wannan
tunani ne mai kyau in dai har an yi shi da kyakkyawar niyya kuma ba kowacce
mace ba ce take da irin wannan tunanin ba. Sai ki godewa Allaah
Dangane da
batun hukuncin yin hakan a shari'ah kuma, wannan ya halatta tunda daman haqqin
ki ne kuma ki ka ga dacewar bada kwanan ga abokiyar zamanki ta yanda tana
dawowa za ta amshe mijin ya koma dakinta
Maganar da
ya fada cewar wannan jahilci ne, a'a ba jahilci bane ba domin kuwa Saudat Bint
Zam'ah (Radiyallahu anha), daya daga cikin matan Annabi (Sallallahu alaihi
wasallam) a lokacin da ta ga ta tsufa kuma tana tsoron kada ya sallame ta sai
tace masa: "Ya Rasulullah, na bawa Aisha gaba daya kwana na". Sai
kuma Annabi (Sallallahu alaihi wasallam) ya aminta da hakan
(Abu Dawood
#2135 sannan kuma Shaikh Muhammad Nasiriddeen al - Albaany ya sahhaha hadisin a
cikin Saheeh Abu Dawood)
Kinga anan
bai fada mata bakar magana ba ballanta kuma ya zage ta saboda ai hakkin ta ne
ba na Nana Aisha din ba
Don haka
wannan kalubale ne ga maza akan yakamata su karanta yanda Annabi (Sallallahu
alaihi wasallam) ya gudanar da mu'amalar sa da iyalan sa
To amman
kinsan dalilin da ya sa mijinnaki yake zagin ki da kuma rashin yaba miki ?
Abu daya ne
!
Qareen !
Qareen shi
ne Aljanin dake jikin sa. Wannan Aljanin shi ne yake son ya ga ya raba aurenku.
Babban burin kafiran Aljanu, Shaidanu, Maridai, Ifritai da kuma oga kwata kwata
wato Iblees shi ne a samu sakin aure tsakanin mata da miji
Kisa, caca,
zina da sauransu duk Allaah yana iya yafewa bayinSa amman yin saki kuwa yana
nufin an dakatar da yiwuwar samun bani Adama wadanda za su shiga Aljannah. Shi
ne babban target din Iblees, a shiga wuta tare da shi saboda shi daman sunyi
hannun riga da shiga Aljannah
An karbo
daga Abdullahi Ibn Mas'ud (Radiyallahu anhu) ya ce: Annabi (Sallallahu alaihi
wasallam) ya ce: "Kowanne dan Adam yana da Aljani (Qareen)"
Sai sahabbai
suka ce: Ya Rasulullah, har kai ?
Sai ya ce:
"Har ni, saidai ni Allaah ya taimake ni nawa ya musulunta kuma yana
kwadaitar da ni ayyukan alkhairi ne"
(Sahihu
Muslim #2814)
Musamman
Imam an - Nawawy ya kulla babi mai suna: "Bab Tahrish al-Shaytan wa
Ba’thihi Sarayahu li Fitnat il-Nas wa anna ma’a kulli insanin Qarin", bi
ma'ana: "Babin sharrin Shaidan da kuma yanda yake tura rundunarsa don su
halakar da yan Adam da kuma hujjar cewar kowa yana da Aljaninsa"
Akwai kuma
hadisin Jabir Ibn Abdullahi (Radiyallahu anhu) wanda ya ce: Annabi (Sallallahu
alaihi wasallam) ya ce: "Al'arshin Iblees tana saman ruwa. Yana tura
rundunoninsa, wanda yafi kusanci dashi shi ne wanda ya zama silar raba
aure"
(Sahihu
Muslim 2813b)
Sannan kuma
a ranar Lahira lokacin da za a jefa dan Adam cikin wuta sai ya zargi abokin
hadin nasa wato Qareen kenan:
( قَالَ قَرِينُهُ
رَبَّنَا مَا أَطْغَيْتُهُ وَلَٰكِن كَانَ فِي ضَلَالٍ بَعِيدٍ )
ق (27) Qaaf
Abõkin haɗinsa ya ce:
"Ya Ubangijinmu! Ban sanya shi girman kai ba, kuma amma ya kasance a cikin
ɓata mai nĩsa."
( قَالَ لَا
تَخْتَصِمُوا لَدَيَّ وَقَدْ قَدَّمْتُ إِلَيْكُم بِالْوَعِيدِ )
ق (28) Qaaf
Ya ce:
"Kada ku yi husũma a wuriNa, hakika tuni na gabatar muku da gargadin
azaba."
( مَا يُبَدَّلُ
الْقَوْلُ لَدَيَّ وَمَا أَنَا بِظَلَّامٍ لِّلْعَبِيدِ
)
ق (29) Qaaf
"Ba a
musanya magana a wuriNa, Kuma Ban zama Mai zãlunci ba ga bãyiNa."
Ibn Khathir
(Rahimahullah) ya ce: "Abdullahi Ibn Abbas, Qatadah, Mujahid da wasun su
duk sun ce wannan Qareen din na nufin abokin hadi ko kuma Aljanin kowanne
mutum"
To kinga
anan idan mijin naki bai canza halin sa ba akwai yiwuwar Qareen dinsa zai
nasara akansa, yanda za su shiga wuta tare. Allaah ya kiyaye. Musamman ma idan
ya zamana ba ya adalci a tsakanin ke da ragowar matan sa. Ana gudun kada ranar
lahira ya tashi da cutar barin jiki (Paralyze) kamar yanda Annabi (Sallallahu
alaihi wasallam) ya fada a cikin Sahihayn
Akwai
hadisin Abdullahi Ibn Umar (Radiyallahu anhu) wanda ya ce: "Annabi
(Sallallahu alaihi wasallam) ya ce: "Idan dayanku yana sallah ka da ya
bari wani ya gifta masa, idan duk da haka mutum ya yi kokarin giftawa to ka
yake shi domin kuwa yana tare da Qareen ne"
Imam ash -
Shawkany (Rahimahullah) ya ce: "Kalmar Qareen, a cikin kamus din larabci
na nufin abokin hadi, kuma abune sananne cewar ko da yaushe shaidan yana tare
da dan Adam ne, duk inda zai je baya barin sa"
* (Nayl
al-Awtar, 3/7)*
Muna rokon
Allaah ya sa wannan sakon yaje kunnuwan mazaje musamman wadanda suke zagi da
kuma rashin nuna kulawa ga matan su. Ku tuna cewar shaidan ne yake son raba ku
la'akari da ai lokacin da kana neman auren ta tarairayarta kake harma ba ka son
ka bata mata rai to don me kuma bayan shekara da shekaru da shafa fatihar
Daurin auren ku kake son Qareen ya rusa niyyarka ta aure don kiyaye mutuncin
kanka
Annabi
(Sallallahu alaihi wasallam) ba irin wannan rayuwar ya yi da iyalansa ba.
Wannan lamarin qalubale ne babba ga maza baki daya !
Zan so
kowanne Namiji ya karanta littattafan nan guda 3 kacal. In dai ka ga rayuwar ka
ba ta sauya ba to ba ka karanta su bane ba:
1)
"Shama'ilil Muhammadiyya" na Abu Isah at - Tirmidhi
2) "How
He Treated Them" by Shaikh Muhammad Saleh al - Munajjid
3) "Men
Around The Messenger" by Khalid Muhammad Khalid
Wallaahu
taala aalam
Masu buqatar
shiga Telegram Class na littafin da muka fara: "KURA KURAI 100 A CIKIN
SALLAR MU", ku shiga Telegram dinku kuyi searching:
USMANNOOR
ACADEMY
Amsawa:
Usman
Danliti Mato (Usmannoor_Assalafy)
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.