HUKUNCIN KALLON TSIRAICI GA MAI KARƁAR HAIHUWA
TAMBAYA
(250)❓
Aslm malam an tashi lpya, kallon tsiraici babu kyau,a musulunci, kuma haramcin ne, malam idan kuma aikin asibiti kake yi kuma kana (conducting labour) karban haifuwa fa🤔🙏
AMSA❗
Waalaikumus
salam
Tabbas
kallon tsiraici haramun ne idan ka dauke wanda ke tsakanin mata da miji sai
kuma na larura kamar irin na karbar haihuwa din har bukatar hakan ta taso
Annabi
(Sallallahu alaihi wasallam) ya ce: "Al'aurar namiji tana farawa ne daga
cibiya zuwa gwiwa"
(Ahmad, Abu
Dawud da Daruqutni)
Haka kuma
gaba ki daya mace al'aura ce kuma ya zama dole ta rufe jikinta in dai tana
gaban wadanda ba muharramanta ba saboda fadin Allaah Azzawajallah:
ۚ وَإِذَا سَأَلْتُمُوهُنَّ مَتَاعًا فَاسْأَلُوهُنَّ مِن
وَرَاءِ حِجَابٍ ۚ
الأحزاب (53) Al-Ahzaab
Kuma idan zã
ku tambaye su waɗansu kãyã, to, ku tambaye su daga bãyan shãmaki.
Da kuma
hadisin: "Dukkan mace al'aura ce"
(Tirmidhi da
isnadi sahihi)
Sai dai da
fuskarta da kuma tafukan hannayenta wadannan biyun ba al'aura bane ba
Idan ya
zamana babu wata larura ta rashin lafiya to haramun ne ganin al'aurar ta amman
idan akwai larura kamar ta karban haihuwa wanda ba makawa sai an ga al'aurar ta
to wannan ya zama larura saidai kuma duk da haka za a iya kalla ne kadai da
manufar karbar haihuwar bawai wata mummunar manufa ba
Shi ya sa malamai
suke bada shawara akan mata su dage da karatun bangaren lafiya ko don irin
wannan matsalar wadda babu dadi ace namiji ne zai karbi haihuwar mace
Wallaahu
taala aalam
Masu bukatar
shiga Telegram Class na littafin "KURA KURAI 100 A CIKIN SALLAR MU",
ku shiga Telegram kuyi searching:
USMANNOOR
ACADEMY
Amsawa:
Usman
Danliti Mato (Usmannoor_Assalafy)
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.