TAMBAYA (213)❓
Malam Dan Allah a taimaka min da addu'a Wadda zan yi da dare ya yi tsoro ke taso min wlh
AMSA❗
Tsoro
Halitta ce kowa yanada
Amman ko
kinsan da cewar ana iya sarrafa tsoro ?
Kuma ba
wahala. Kenan abin sa Kai ne kawai
Tsoro da
Larabci shi ake Kira da Khauf Kuma ya rarrabu gida 3:
1) Haram
(Haramun)
2) Mubah (Ba
dole ba) da kuma
3) Wajib
(Dole)
Inda zai
zama Haramun shine tsoron da zai kai ka ga fidda tsammani daga Rahamar Allaah
ko Kuma tsoron Aljani zai iya cutar dakai
Inda Kuma
zai zama Mubah bi ma'ana ba dole ba shine: Aure, Tafiya, Kwanciya bacci, Cin
abincin halal, saka tufa ta halal da sauransu
Sai Kuma
Wajib wato abinda ya zama dole. Shi ma Kuma ya rarrabu gida 2 ne: Fard al-ayn
(kamar: Sallah, Azumi, Zakkah) da Kuma Fard al-kifayah (kamar: binne mamaci)
akwai Kuma Wajib 'ayn (Kamar Neman ilimi dogaro da hujjar Aya ta farko da aka
fara saukarwa a Qur'ani) da Kuma Wajib kifaya (Kamar gina masallachi)
Akwai Kuma
tsoron na Dabi'a Shima ya halatta kamar tsoron Mutuwa, Wuta, Maqiyi, Zaki ko
Maciji (Kamar yanda Annabi Isah Alaihis Salam yaji tsoron sanda lokacinnan da
ta zama Macijiya)
Matakin
farko na rabuwa da tsoro shine jin tsoron Allaah a matsayin Sa na Mahalicci
Domin kuwa
yawan aikata Zunubbai na fili da Kuma musamman na boye (daga Kai sai Allaah)
yana da alaqa da rashin jin tsoron Allaah Al-Jabbaru yayinda Kuma ya zamana
mutum ba zai ji tsoron al-Khaliqu ba to sai Mai halittar ya hadashi da tsoron
Makhluqai (wato ababen halitta) wannan dalilin ne ya sa kike yawan jin tsoron
Mafita anan
shine ki ji tsoron Allaah shi kadai sai ya cire Miki tsoron halittunSa
Ki yawaita
karanta Suratu ad-Dhuha domin kuwa dalilan saukar ta (asbabun nuzul) yanada
alaqa da damuwa da Ma'aiki Sallallahu alaihi wasallam ya shiga sakamakon
tsagaita yi masa wahayi. Shiyasa Allaah Azzawajallah ya ce:
( مَا وَدَّعَكَ رَبُّكَ
وَمَا قَلَىٰ )
الضحى (3) Ad-Dhuhaa
Ubangijinka
bai yi maka bankwana ba, kuma bai ƙĩ kaba.
Sai kuma ki
tuno da addu'ar da Annabi Sallallahu alaihi wasallam yake yawaita karantawa
akan tsoro
اَللّهُمَّ إِنِّي أَعُوذُ بِكَ مِنَ الْهَمِّ وَالْحُزْنِ،
والْعَجْزِ والكَسَلِ والبُخْلِ والْجُبْنِ، وضَلْعِ الدَّيْنِ وغَلَبَةِ الرِّجَالِ.
Allahumma
innee a'oothu bika minal-hammi walhuzn, wal'ajzi walkasali walbukhli waljubn,
wadal'id-dayni waghalabatir-rijal.
Ya Allah!
Ina neman tsarinka daga damuwa; da bakin ciki, da gajiyawa, da lalaci, da rowa,
da rinjayen mazaje.
Hisnul
Muslim
Ki yawaita
karanta addu'ar Ma'abocin kifi wato Annabi Yunus Ibn Mat'a, a lokacin da kifi
ya hadiyeshi sai ya ce:
"La'ilaha
illa antas subhanaka inni kunta minazzalimeen"
Kuma ki
yawaita karanta addu'ar da Annabi Ibrahim Alaihis Salam ya karanta a likacin da
za a jefa shi cikin Wuta:
"Hasbiyallahu
wani'imal wakeel"
Da ni dake
mu ji tsoron Allaah a cikin ayyukan mu na fili da Kuma musamman na boye (Kamar
lokacin da muke danna waya mu kadai ba tareda wani ya ganmu ba). Duk da cewar
ba Makhluqin da yake garinmu to ammanfa al-Khaliqu yana ganin mu Sarai
Ya Allaah ka
yafe mana
Wallaahu
ta'ala a'alam
*Amsawa:_
Usman
Danliti Mato (Usmannoor_Assalafy)
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.