TAMBAYA (223)❓
Nifa mlm abun da nake son yagane idan ya yi sunna da matarshi yaje ya kawar da najasa Amman bashi sai lokacin sallah ya yi sai ya yi wanka yaje sallah da asuba
AMSA❗
Ya halatta
ya jinkirta dinnan
Musamman ma
idan ya zamana babu ruwa ko kuma idan ya taba ruwan zai cutu
Mustahabbi
ne da ke da mijin kuyi akwala kafin ku koma bacci. Wannan shi ne fahimtar
ijma'in malamai. Haka kuma Imam an - Nawawy (Rahimahullah) ya ce: Akwai
maganganun malamai akan wannan mas'ala
(Al-Kafi,
1/173; al-Muhadhdhab, 1/33; al-Mughni, 1/229)
A takaice
dai ba damuwa bane ba don mijinnaki ya kwana da janaba, domin kuwa Nana Aisha
(Radiyallahu anha) ta ce:
"Idan
Annabi (Sallallahu alaihi wasallam) yana son yin bacci alhalin a jikinsa akwai
janaba, yana wanke gabansa ne sannan sai ya yi alwala irin wadda yake idan zai
yi sallah"
(Bukhari da
Muslim)
Haka kuma
Abdullahi Ibn Umar (Radiyallahu anhum) ya ce: Sayyadina Umar ya ce: Ya
Rasulullah, shin ya halatta dayanmu ya yi bacci alhalin yana cikin janaba ?
Sai Annabi
(Sallallahu alaihi wasallam) ya ce: "Eh, idan ya yi alwala ba"
(Muttafaqun
alaihi)
Hikimar yin
alwalan kafin a kwanta shi ne: hakan yana rage janabar kuma jiki sai yafi samun
nutsuwa
Tuntuni muka
wuce wannan karatun a cikin littafin: "MU'AMALAR AURATAYYA A
MUSULUNCI", don haka karki damu idan har baiyi wankan da wuri ba
Saidai duk
da haka anfi son a dinga wankan akan lokaci saboda ba a son ko da yaushe mutum
ya kasance cikin janaba ko don tuna cewar Malaikun Rahama ba sa zuwa gidan da
akwai mutum mai najasa har fa sai ya gusar da ita
Wallaahu
taala aalam
Amsawa:
Usman
Danliti Mato (Usmannoor_Assalafy)
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.