Ticker

6/recent/ticker-posts

Taimamar Marar Lafiya

TAMBAYA (222)

Assalamu alaikum warahmatullah malam yahidima damu Ubangiji ya saka dagidan aljannah firdaus mlm ina tare damara lfy jikinta akwai fitsari bata iya komai sai ammata amma tana hankalinta za a mata taimamane ko alwala,Allah yakara lfy

AMSA

Taimama za ta dinga yi in Sha Allaah saboda fadin Allaah Azzawajallah:

( يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا لَا تَقْرَبُوا الصَّلَاةَ وَأَنتُمْ سُكَارَىٰ حَتَّىٰ تَعْلَمُوا مَا تَقُولُونَ وَلَا جُنُبًا إِلَّا عَابِرِي سَبِيلٍ حَتَّىٰ تَغْتَسِلُوا ۚ وَإِن كُنتُم مَّرْضَىٰ أَوْ عَلَىٰ سَفَرٍ أَوْ جَاءَ أَحَدٌ مِّنكُم مِّنَ الْغَائِطِ أَوْ لَامَسْتُمُ النِّسَاءَ فَلَمْ تَجِدُوا مَاءً فَتَيَمَّمُوا صَعِيدًا طَيِّبًا فَامْسَحُوا بِوُجُوهِكُمْ وَأَيْدِيكُمْ ۗ إِنَّ اللَّهَ كَانَ عَفُوًّا غَفُورًا )

النساء (43) An-Nisaa

"Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku kusanci salla alhãli kuwa kuna mãsu mãye, sai kun san abin da kuke faɗa kuma haka idan kuna mãsu janaba, fãce mai ƙẽtare hanya, har ku yi wanka. Kuma idan kun kasance majinyata, ko kuwa a kan tafiya ko kuwa wani daga cikinku, idan ya zo daga kãshi, kõ kuwa kun shãfi mãtã ba ku sãmi ruwa ba, to ku nufi, fuskar ƙasa mai kyau, ku yi shãfa ga fuskokinku da hannuwanku. Lalle ne Allah Yã kasance Mai yãfwa Mai gãfara"

Idan ba za ta iya ba sai a dinga yi mata sannan kuma za ta iya sallar a zaune ko a kwance ko kuma idan duk ba za ta iya ba sai ta dinga kudurcewa a zuciyarta kamar yanda ya tabbata a cikin littafin: "Sifatu Salatin Naby"

Wannan duk saukine daga addinin Musulunci kamar yanda muka yi bayani a lecture mu ta farko cikin littafin: "KURA KURAI 100 A CIKIN SALLAR MU"

Wasu suna ganin idan suna kula da mara lafiya ba sai ya yi sallah ba alhalin yin sallah a lokacin ta dole ne, ga mara lafiya, matafiyi ko mazaunin gida. Allaah Azzawajallah ya ce:

( فَإِذَا قَضَيْتُمُ الصَّلَاةَ فَاذْكُرُوا اللَّهَ قِيَامًا وَقُعُودًا وَعَلَىٰ جُنُوبِكُمْ ۚ فَإِذَا اطْمَأْنَنتُمْ فَأَقِيمُوا الصَّلَاةَ ۚ إِنَّ الصَّلَاةَ كَانَتْ عَلَى الْمُؤْمِنِينَ كِتَابًا مَّوْقُوتًا )

النساء (103) An-Nisaa

Sa'an nan idan kun ƙãre salla, to ku ambaci Allah tsaye da zaune da a kan sãsanninku. Sa'an nan idan kun natsu, to, ku tsayar da Salla. Lalle ne salla tã kasance a kan mũminai, farilla mai ƙayyadaddun lõkuta.

Shaykh al-Islam Ibn Taymiyah (Rahimahullah), a cikin Majmoo‘ al-Fatawa (22/293) dinsa ya ce:

"Ya halatta mara lafiya ko matafiyi ya hade sallar azahar da la'asar ko magariba da Isha'i kamar yanda ya halatta a hadesu lokacin da ake ruwan sama. Duk wannan sauki ne ga al'ummah"

Haka kuma Committee Fatawa al-Lajnah ad-Daa’imah, a cikin mujalladi na 8 shafi na 83, sunce ya halatta mara lafiya ya yi sallah a tsaye idan ba zai iya ba ya yi a zaune, idan ba zai iya ba sai ya yi a kwance sannan da mara lafiya da matafiyi za su iya hade sallolin Azahar da La'asar da kuma Magariba da Isha'i

Wallaahu taala aalam

Amsawa:

Usman Danliti Mato (Usmannoor_Assalafy)

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam 

Post a Comment

0 Comments