TSAKANIN SAHIHUL BUKHARI DA SAHIHU MUSLIM DA LITTAFIN "THE ORGANON" NA ARISTOTLE
Yauzu me kake ganin zai faru idan muka ce karya ne, Aristotle ba shi da wani littafi mai suna The Organon, kawai wani ne ya sharara karya, ya kirkiri littafin ya jingina masa shi?
Yau tsakaninmu da Aristotle kusan shekara 2400 ne.
Don haka ta yaya za mu iya tabbatar da cewa; wannan littafi na Aristotle ne?
Ko shakka babu wadanda suka yi Imani da Aristotle
suke karanta littatafansa da maganganunsa suke girmama su za su ji ras! Har su
ce: ta yaya za a yi kokarin inkarin littafin da mutane suka hadu a kan tabbatar
da shi?!
To idan har za ka yarda da littatafan Aristotle,
wadanda tsakaninmu da shi yau kusan shekara 2400, kuma idan an ce: ana so a
tabbatar da dangantuwar littafin gare shi babu hanyar da za a bi wajen iya
tabbatar da hakan face kawai abin da aka sani bisa gado, cewa; littatafansa ne.
Amma abin mamaki, mai tabbatar da wannan littafi
na Aristotle shi ne kuma mai inkarin "Sahihul Bukhari da Muslim",
alhali tsakaninmu da su shekara 1200 ne. Kuma Hadisan Annabi (saw) sun samu
kulawar da babu wasu maganganu da suka samu irin wannar kulawa. An samu manyan
Malaman Muslunci wadanda suka sadaukar da rayuwarsu wajen kiyaye Hadisan da yi
musu Hidima. Inda suka samar da ka'idoji da sharuda masu karfin gaske wajen
tantance Hadisan. Suna da wani ilimi da ake kira da "Ilmur Rijaal",
ilimin da yake mai da hankali a kan bin diddigin Maruwaitan Hadisi da tantance
gaskiyarsu da amanarsu da karfin haddarsu da iya rike magana da ruwaito ta bisa
yadda take, ba tare da canji ba.
Haka kuma Malaman suka himmatu wajen rubuta
Hadisan cikin littatafai, wanda ya kasance tun a rayuwar Annabi (saw), inda ya
yi izini ma daya daga cikin Sahabbai da rubuta Hadisansa. Haka kuma cikin
ilmuka da Malaman Hadisin suka tanada don kwalkwale ingancin Hadisi akwai
"Ilmul Ilal", wato ilimin sanin boyayyiyar matsala da illa da take
cikin Hadisi. Saboda ta yiwu a samu Hadisi, a zahirinsa aga kamar ingantacce ne
alhali yana da boyayyar matsala. Amma Malaman Hadisi ba su yi kasa a guiwa ba
wajen bin diddigi da binciken kwakwaf ma Hadisan, don banbance Hadisan da suka
tabbata daga Annabi (saw), daga wadanda babu tabbacin hakan.
Akwai wata ja'irar shubuha da mabarnata suke
amfani da ita idan suna son boye gaskiya, su tallata barnarsu ga jahilai, sai
su ce: ai akwai siyasa a cikin kaza da kaza.. To hatta rubuta Hadisan Annabi
(saw) sai da aka jefe shi da wannar ja'irar shubuha. Aka ce: ai Sarakuna ne
suka sa aka kirkira musu Hadisan don biyan bukatunsu na Mulki, aka rubuta su
cikin littatafai. To ta yaya mai hankalin da ya san cewa; Imamu Malik wanda ya
wallafa Muwadda' an yi masa bulala. Imamu Ahmad mai littafin al-Musnad an yi
masa bulala, an daure shi a kurkuku. Imamu al-Bukhariy mai littafin
"Sahihul Bukhari", an kore shi daga garinsu. Duka wadannan Malamai da
ire - irensu sun fiskanci hakan ne ta bangaren Sarakunan zamaninsu.
To ta yaya mai hankalin da ya san wannan zai yarda
da waccar ja'irar shubuha ta siyasantar da Addini, wacce mabarnata suke amfani
da ita, don boye gaskiya, da tallata barnarsu a tsakanin jahilai?!
To idan kuma aka ce: To ina asalin littatafan da
wadancan Malamai suka rubuta da hanunsu?
Idan ba a samu ba, to kenan zai zama wasu ne suka
rubuta, suka jingina musu su.
To sai mu koma kan maganar farko, ta magana a kan
littatafan Aristotle, ina asalin kwafi da Aristotle ya rubuta da hanunsa?
Idan babu, ta yaya aka yarda da littatafan, duk da
cewa; ba a samu asalin kwafi na farko ba?
Kuma yanzu littatafan nasa da suke hanu duka
tarjama aka yi daga yarensa na asali zuwa wasu yarukan daban, kuma kowa ya san
yadda ake iya samun canje-canjen ma'ana a dalilin Tarjama. Saboda haka idan an
ce: ai almajiransa ne suka nakalto daga gare shi, su ma almajiransu suka
nakalto daga gare su, haka har aka rubuta su, har suka iso gare mu, to haka su
ma Littafan Hadisi suke, irin su Bukhari da Muslim da sauransu. Duk da cewa; ba
za ma a hada riwayar littatafan Aristotle da littatafan Hadisi ba, saboda
Muwadda' Malik, kwafi mafi tsufa da aka samu tsakaninsa da Malik kusan shekara
100 ne kacal. Haka Sahihul Bukhari ma. Amma duk da haka kowane littafi an
ruwaito shi ne da Isnadi tiryan-tiryan har zuwa kan mai littafin. Shi kuma da
Isnadinsa a rubuce a kowane Hadisi har zuwa Annabi (saw). Sabanin littatafan
Aristotle, wanda tsakaninsa da tsohon kwafi na littafin nasa ya kai shekara
1000 bayan mutuwarsa. Amma duk da haka masu shakka a kan littatafan Hadisi ba
za ka samu suna shakka a kan tabbacin littatafan Aristotle ba, duk da banbance
- banbancen yaruka da Tarjama da aka samu, da kuma yadda masu Tarjamar
littatafan suke tassarufi da rubuta maganganunsa da ma'ana ba da lafazinsa ba,
da sauran wasu abubuwa masu tasiri wajen canza ma'ana, kuma wadanda za su sa a
yi shakka wajen ingancin Nassin da aka nakalto.
A takaice, duk mai basira idan ya yi nazarin
littatafan Hadisi masu inganci zai ga cewa; babu yadda za a yi wata shubuha ta
sukarsu ta yi tasiri.
✍️ Dr. Aliyu Muh’d Sani (H)
Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.