YADDA ZA KA BI MAZHABAR MALIKIYYA IDO BUƊE
Asali ba a wajabta mana bin kowa ba sai bin
Alkur’ani da Sunna, da Ijma'in Muminai. Shi ya sa Imam al-Shafi'iy ya ce
"إنما العلم اللازم الكتاب والسنة، وعلى كل مسلم اتباعهما.
قال: فتقول أنت ماذا؟
قلت: أقول ما كان الكتاب والسنة موجودين فالعذر عمن سمعهما
مقطوع إلا باتباعهما".
الأم للشافعي (7/ 280)
"Kawai Ilimin dole a kan mutum shi ne
Alkur'ani da Sunna, wajibi ne a kan kowane musulmi ya bi su.
Sai aka tambaye shi: to kai miye ra'ayinka?
Sai na ce: matukar Alkur'ani da Sunna suna nan to
an yanke hanzari ga duk wanda ya ji su dole sai dai ya bi su".
To ka ga Imam Shafi'iy, almajirin Imam Malik ne,
kuma jagoran Mazhabar Shafi'iyya, amma yake nuna cewa; matukar ka samu Aya ko
Hadisi a kan mas'ala, to ba ka da sauran uzuri, dole ne ka bi su, ka yi aiki da
su.
To yanzu don Allah idan ka samu Hadisi tabbatacce,
sai ka ki binsa, sai ka bi ra'ayin Malik, miye sunanka?
Kafin mu rada maka suna bari ka ji matsayinka daga
maganar Imam Malik, inda aka ruwaito
"عن معن بن عيسى قال: سمعت مالك بن أنس يقول: «إنما أنا بشر،
أخطئ وأصيب، فانظروا في رأيي؛ فكلما وافق الكتاب والسنة فخذوا به، وكلما لم يوافق
الكتاب والسنة فاتركوه».
جامع بيان العلم وفضله (1/ 775)
"Daga Ma'an bn Isa, ya ce: Na ji Malik bn
Anas yana cewa: Ni mutum ne, ina yin dadai kuma ina kuskukre, don haka ku yi
nazari a cikin ra'ayoyina, duk abin da ya dace da Alkur'ani da Sunna to ku yi
riko da shi, duk abin da bai dace da Alkur'ani da Sunna ba to ku bar shi".
To yanzu idan ka ga Hadisi ya tabbata, sai ka doge
a kan ra'ayin Malik ko Malikiyya, shin ka yi biyayya wa Imam Malik a cikin
wannar maganar tasa?
Don haka sunanka ya zama MAI SABA WA MALIK!
Ko shi Imam Malik din Alkur'ani da Sunna yake bi,
idan ka ga ya saba ma wani Hadisi to imma bai samu Hadisin ba ne, ko kuma ya
samu Hadisin, amma ya saba aikin mutanen Madina ingantacce, musamman idan
Hadisin mutanen wani yankin ne can daban, musamman Iraq. Ko kuma Hadisin bai
inganta a wajensa ba. Amma da zaran ya samu Hadisin, kuma ya tabbata a wurinsa
to nan da nan zai bar ra'ayinsa, ya karbi Hadisin ya yi aiki da shi.
Ga misali kamar haka
Imam Ibnu Abdilbarr ya ce
"ذكر أحمد بن وهب قال: حدثني عمي عبد الله بن وهب قال: سئل
مالك عن تخليل أصابع الرجلين في الوضوء، فقال: ليس ذلك على الناس.
فأمهلته حتى خف الناس عنه، ثم قلت له: يا أبا عبد الله،
سمعتك تفتي في مسألة عندنا فيها سنة، قال: وما هي؟ قلت: حدثنا ابن لهيعة والليث بن
سعد عن يزيد بن عمرو المعافري عن أبي عبد الرحمن الحبلي عن المستورد بن شداد
القرشي قال: "رأيت رسول الله يتوضأ فيخلل بخنصره ما بين أصابع رجليه".
قال فقال لي مالك: إن هذا لحسن، وما سمعت به قط إلا الساعة.
قال ابن وهب: ثم سمعته بعد ذلك يسأل عن تخليل الأصابع في
الوضوء فيأمر به.
وروى غيره عن ابن وهب: فرأيته يعمل به، ولم يقل بأمره".
التمهيد لما في الموطأ من المعاني والأسانيد (24/ 258 -
259) اختلاف أقوال مالك وأصحابه (ص: 40)
"An ruwaito daga Abdullahi bn Wahab ya ce: an
tambayi Malik a kan tsettsefe yatsun kafa a alola. Sai ya ce: babu shi a kan
mutane.
Sai Ibnu Wahab ya ce: sai na bari sai da mutane
suka watse, sai na ce masa: Ya Abu Abdillah, na ji ka kana fatawa a wata
mas'ala, alahali muna da Hadisi a kanta.
Sai Malik ya ce: wane Hadisi ne?
Sai na ce: Ibnu Lahi'ah da al-Laith bn Sa'ad sun
ba mu labari daga Yazid bn Amri al-Mu'afiriy, daga Abu Abdirrahman al-Hubulliy,
daga al-Mustaurid bn Shaddad al-Qurashiy, ya ce: "Na ga Manzon Allah yana
alola yana tsettsefe yatsun kafansa da 'yar karamar yatsar hanunsa".
Sai Malik ya ce min: Lallai wannan Hadisi ne mai
kyau, amma ban taba jinsa ba sai yanzu.
Ibnu Wahab ya ce: sai daga baya na ji ana
tambayarsa game da tsettsefe yatsun kafa yana yin umurni da shi.
A wata riwayar kuma cewa ya yi: sai ya gan shi
yana aiki da Hadisin, amma bai fadi cewa yana umurni da shi ba.
To ya kai dan Malikiyya, ka ga dai yadda Imamu
Malik din namu yake da Hadisi, matukar Hadisi ya tabbata a wajensa to zai yi
aiki da shi.
Saboda haka wannan shi yake nuna yadda Ahlus Sunna
suke bin Mazhaba, da zaran Hadisi ya tabbata to sukan ajiye ra'ayin Malikiyya
wanda ya saba wa Hadisin.
Don haka yadda ake bin Malikiyya ido bude, shi ne
ka sanya Alkur'ani da Hadisi su ne abin bi, don haka da zaran ka ga Hadisi ya
inganta a wata mas'ala, kuma akwai banbanci tsakanin Hadisin da ra'ayin
Malikiyyar, to ka bar ra'ayin Malikiyyan, ka yi riko da Hadisin, ka yi aiki da
shi.
Kuma fa kar ka manta, ba dukkan ra'ayoyin
Malikiyya a yau su ne ra'ayin Malik ba, akwai ra'ayoyi da yawa Malaman baya ne
suka yi Ijtihadi suka tabbatar da su. Don haka ta yaya za ka gabatar da ra'ayin
wani wanda ba Malik ba a kan Hadisi, alhali shi ma Malik din cewa ya yi: idan
ra'ayinsa bai dace da Alkur'ani da Sunna ba to kabar shi, to ina kuma ga
ra'ayoyin Malaman da suka zo bayan Malik?!
Shi ya sa mu 'yan Malikiyya muke jin takaici idan
muka ji mutum yana raya bin Malikiyya, amma kuma ya saba wannan Manhaji, ya
koma taqlidanci da ta'assubanci wa Mazhabar.
✍️ Dr. Aliyu Muh’d Sani (H)
Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.