'YAR'UWA KI JI TSORON ALLAH!
Akwai wata mummunar Fikra wacce take ta kara yaduwa a cikin mutane, musamman mata da kuma matasa maza, fikrar da take da tushe daga Akidar Murji'a. Amma yanzu an dauko ta ne cikin sabuwar riga, daga kungiyoyin Fikrorin Turawa, wadanda 'Yan Boko Aqida suka yi dakonsu, suke yada su cikin al'ummar Musulmi.
Wannar fikra ita ce fikrar bai ma kowa 'yancin
aikata abin da yake so, cikin aiyukan da Allah ya hana aikatawa, na alfasha da
munkari.
A yanzu ba dama ka yi inkarin mummunan aiki ga
wata mace, kamar dora hotunan tsiraici, ko bidiyon rawa a dandalin sada
zumunta, face ta yi maka martani da cewa
"Kabarinka daban, nawa daban".
Ko ta ce
"Kar ka shiga rayuwata, ka yi harkarka, na yi
nawa".
Ko ta ce
"Ni ban shiga rayuwar kowa ba, kar kowa ya
shiga rayuwata".
Ko ta ce
"Ku kyale kowa ya yi rayuwarsa yadda yake
so".
Ko kuma ta ce
"Imani fa a zuciya yake".
Ko ta ce
"Kai wa ya san abin da kake aikatawa a
boye".
Ko ta ce
"Rahmar Allah tana da fadi".
Da sauran ire-iren wadannan kalamai, suna nan da
yawa.
To ya ke 'yar'uwa, na san dai kin san cewa Allah
ya haramta alfasha da munkari.
Kuma kin san Allah ya tanadi azaba ta Lahira a kan
haka, ko ma tun daga nan Duniya.
Kuma kin san mutuwa ba ta sallama, balle bayar da
sanarwa idan za ta zo.
Kuma kin san Allah ya wajabta hani a kan mummunan
aiki da inkarin munkari.
Kuma kin san bayyana mummunan aiki da sabo a fili
suna cikin aiyukan da Allah ya fi yin fushi da su, kuma yake hana afuwarsa ga
masu aikatawa.
'Yar'uwa, ko kin san dalilin da ya sa Allah ya
tsine wa Kafiran Bani Isra'ila kuwa?
Ko kin san dalilin da ya sa Allah ya daukaka
al'ummar Annabi Muhammad (saw), ya fifita ta a kan sauran al'ummomi kuwa?
Allah ya tsine wa Kafiran Bani Isra'ila ne saboda
ba sa hana juna aikata munanan aiyuka.
Allah ya daukaka al'ummar Annabi Muhammad (saw)
ne, ya fifita ta a kan sauran al'ummomi saboda suna umurni da kyakkyawa, suna
hani ga mummuna, suna Imani da Allah?
To idan fa muka canza, muka dena umurni da
kyakkyawa, da hani ga mummuna, to fa zamu rasa falalar al'ummar Annabi (saw),
mu cancanci irin tsinuwar da Allah ya yi wa Kafiran Bani Isra'ila.
Haba 'Yar'uwa, ko ke ma kina da mummunar Akidar
nan ce, ta cewa: masifun da suka same mu a yau, na Kidnapping, rashin tsaro,
bala'in talauci da tsadar rayuwa da samun shugabanni marasa tausayi ba su da
alaka da munanan aiyukan da muke aikatawa ne?!
Allah fa ya fada mana a wurare da yawa a cikin
Alkur'ani, cewa; bala'o'i da suke faruwa sababinsu shi ne miyagun aiyukan da
muke aikatawa ne.
Annabi (saw) ya yi mana misali mai kyau don mu
gane. Wato misalin masu hana ki aikata munanan aiyuka na alfasha da munkari, ta
yadda ya yi mana bayanin cewa; kamar fasinja ne a cikin jirgin ruwa mai hawa
biyu, hawa na sama da na kasa. To idan mutanen hawa na kasa suna bukatar ruwa,
a maimakon su hawo sama, su samu hanyar fita su debo ruwan, sai suka ce: bari
mu bula jirgin ta kasa, ruwan ya shigo mana ba tare da mun damu wadanda suke
hawa na sama da mu ba.
To yanzu, shin ya kamata a kyale wadanda suke hawa
na kasa su bula jirgin, don ruwa ya shigo musu?
Idan fa aka kyale su suka bula jirgin, to ruwa zai
shiga jirgin ya cika shi, daga nan kuma sai jirgin ya yi kasa ya nitse a Teku,
kowa ma ya mutu a huta.
Lallai hani a kan munanan aiyuka shi yake kare
al'umma daga halaka da bala'o'i iri-iri.
Don haka 'yar'uwa ki ji tsoron Allah! Ki dena
aikata mummunan aiki, balle ki yada, ballantana kuma har ki yi mummunan martani
ga mai hana ki aikatawa.
✍️ Dr. Aliyu Muh’d Sani (H)
Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.