TAMBAYA (224)❓
Assalamualaikum. Mln ya hukuncin Wanda yake tsallake masallacin dake unguwarsa ya yafi wani masallacin sallar tarawiyyi ko tahajjud
AMSA❗
Ya halatta
ka je kowanne masallachi amman ya zamana limamin yana sallah ne irin yanda
Annabi Sallallahu alaihi wasallam ya koyar dogaro da hadisin: "Kuyi sallah
kamar yanda kuka ga ina yi"
(Bukhari da
Muslim)
Inda zaka
zamo abin tuhuma shi ne idan kana cikin masallachin aka kira sallah sai kuma ka
fita hakanan ba tare da wani dalili ba. Wannan ka aikata laifi saboda hadisi na
10,946 dake cikin Musnad na Imam Ahmad (Rahimahullah) wanda Abu Hurairah
(Radiyallahu anhu) ya ce: Annabi (Sallallahu alaihi wasallam) ya umarce mu da
kada mu fita daga masallachi idan an kira sallah har sai anyi sallar tare da mu
Shu’ayb
al-Arna’oot ya sahhaha hadisin a cikin Tahqeeq al-Musnad din sa
Ga kuma
hadisin Abu’l-Sha’tha’ wanda ya ce: Muna tare da Abu Hurairah bayan an kammala
kiran sallah a masallachi sai wani mutum ya tashi ya fita daga masallachin, sai
Abu Hurairah ya dinga kallon sa har ya fice sai ya ce: Wannan mutumin ya
bijirewa umarnin Abul Qasim (Sallallahu alaihi wasallam)
Dangane da
fitowa kai tsaye daga gida zuwa masallachi kuma, akwai garabasar samun lada
dayawa idan aka je masallachi mai nisa saboda duk sanda kayi taku daya Allaah
zai sa a rubuta maka lada sannan a kankare maka zunubi daya kamar yanda muka
karanta hadisin a cikin littafin SIFATU SALATIN NABY
Shiyasa
malamai sukai magana akan illar yawaita gina masallatai da yawa a anguwa daya
musamman na Juma'a domin kuwa hakan na iya janyo rarrabuwar kai da kuma bude
kofar kungiyanci
Duk da cewar
wasu suna ginawa ne don a raya dakunan Allaah to amman anan sai malamai suka ce
mutum ya zabi masallachin da aka fi cika domin kuwa munada hadisin Ubayy Ibn
Ka'ab (Radiyallahu anhu) wanda ya ce: Annabi (Sallallahu alaihi wasallam) ya
ce: "Mutum ya yi sallah tareda wani shi yafi akan ya yi shi kadai, yin ta
da wasu su biyu shi yafi akan ya yi da mutum daya, iya adadin yawan masu sallah
shi ne yawan farin ciki da Allaah yake"
Abu Dawood
(554) da an-Nasaa’i (843); Shaikh al-Albaani ya sahhaha shi a cikin Saheeh Abi
Dawood
Wannan kuma
ita ce amsar da Shaykh Muhammad ibn Saalih al-‘Uthaymeen (Rahimahullah) ya
bayar a cikin: Ash-Sharh al-Mumti‘ ‘ala Zaad al-Mustaqni‘ 4/150-151
Wallaahu
taala aalam
Amsawa:
Usman
Danliti Mato (Usmannoor_Assalafy)
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.